• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa duk da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomin, har yanzu da sauran rina a kaba.

 

Haka kuma babbar jam’iyyar adawar ta ce tana nazari kan martanin da suka biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke, tana mai cewa zai yi wuya a iya raba gwamnatin jiha da kananan hukumomi.

  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
  • Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa

Jam’iyyar ta bayyana matsayinta ne ta bakin sakataren yada labaranta na kasa, Honarabul Debo Ologunagba, yayin da yake jawabi ga manema labarai a shalkwatan jam’iyyar na kasa a ranar Lahadin da ta gabata.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Da yake amsa tambaya kan matsayin Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, kan hukuncin kotun koli, Ologunagba ya ce, “Mun yi imanin cewa idan har za a yi wa kananan hukumomi garambawul, ya kamata a yi shi tare da gwamnoni ta yadda za su dace da bukatun gwamnatin tarayya.

 

“Tabbas, na yi imanin hakan ba zai kawo karshen lamarin ba, kamar yadda muke Magana saboda mutanen da ke da alhakkin kananan hukumomi su ne gwamnoni.

 

“Gwamnatin tarayya ba ta ganin mutane a kauyuka, gwamnoni ne suke yin hakan. Don haka idan akwai damuwa, to a hada kai da kananan hukumomi domin amfanar da al’umma, ba wai bukatar wasu ba.

 

“Doka ba ta nuni da abin da ba zai yiwu ba. Idan ta yi nuna da wani abu, za ta fadi hanyar warware duk wata matsala. Na tabbar da cewa mu ba mu ga cewa za a kawo karshen lamarin ba dangane da gudanar da kananan hukumomi.

 

“Gwamnatin jiha tana da alhakkin kan kananan hukumomi. Idan an samu matsala a kananan hukumomi, ba za su kira gwamnatin tarayya ba, za su kira gwamnatin jiha ne.

 

“Don haka dole ne a fahimci cewa gwamnatin jihar tana da hakki kan gudanar da harkokin kananan hukumomi, kuma abin da zai iya aiki a kai shi ne hanya mafi dacewa da za a ba da damar gudanar da ayyukan gwamnatin jihar, tare da gwamnoni da tsarin mulki ya tanadi hadin gwiwar asusun kananan hukumomi.

 

“Kudin tsarin mulki ya tanadar da shi ba gwamnatin tarayya ba ce ta tanadar da shi ba. Don haka a wane lokaci ya zama mara amfani?

 

“Haka kuma, ana ci gaba da tattauna wadannan batutuwa. A matsayinmu na jam’iyya, za mu yi ta tattaunawa a kai. Za mu kara tattaunawa da gwamnoninmu domin samun mafita.

 

“Na yi imanin cewa a karshe gwamnonin suna da rawar da za su taka dangane da gudanar da harkokin kananan hukumomi, saboda su suke da hakki fiye da kowa. Ina nufin dukkan alhakin gudanarwa, ba na tunanin za a kawo karshen wannan dambarwa.”

 

Mai magana da yawun jam’iyyar PDP ya ce damuwar jam’iyyar a fili take, domin kuwa kananan hukumomi suna da alaka da jihohi saboda sun fi kusa da juna.

 

“Yanzu a matsayinmu na jam’iyya, muna duba wannan hukuncin kotun koli a matsayin wani abun damuwa. Kuma zan fadi haka ne kasancewar gwamnatin tarayya na kokarin sake kirkiro wani tsarin mulkin kama-karya ko karkatar da al’amuran kananan hukumomi, muna ganin hakan zai zama wata hanyar kawo babbar matsala.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECSiyasaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

'Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.