• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa duk da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomin, har yanzu da sauran rina a kaba.

 

Haka kuma babbar jam’iyyar adawar ta ce tana nazari kan martanin da suka biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke, tana mai cewa zai yi wuya a iya raba gwamnatin jiha da kananan hukumomi.

  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
  • Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa

Jam’iyyar ta bayyana matsayinta ne ta bakin sakataren yada labaranta na kasa, Honarabul Debo Ologunagba, yayin da yake jawabi ga manema labarai a shalkwatan jam’iyyar na kasa a ranar Lahadin da ta gabata.

 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Da yake amsa tambaya kan matsayin Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, kan hukuncin kotun koli, Ologunagba ya ce, “Mun yi imanin cewa idan har za a yi wa kananan hukumomi garambawul, ya kamata a yi shi tare da gwamnoni ta yadda za su dace da bukatun gwamnatin tarayya.

 

“Tabbas, na yi imanin hakan ba zai kawo karshen lamarin ba, kamar yadda muke Magana saboda mutanen da ke da alhakkin kananan hukumomi su ne gwamnoni.

 

“Gwamnatin tarayya ba ta ganin mutane a kauyuka, gwamnoni ne suke yin hakan. Don haka idan akwai damuwa, to a hada kai da kananan hukumomi domin amfanar da al’umma, ba wai bukatar wasu ba.

 

“Doka ba ta nuni da abin da ba zai yiwu ba. Idan ta yi nuna da wani abu, za ta fadi hanyar warware duk wata matsala. Na tabbar da cewa mu ba mu ga cewa za a kawo karshen lamarin ba dangane da gudanar da kananan hukumomi.

 

“Gwamnatin jiha tana da alhakkin kan kananan hukumomi. Idan an samu matsala a kananan hukumomi, ba za su kira gwamnatin tarayya ba, za su kira gwamnatin jiha ne.

 

“Don haka dole ne a fahimci cewa gwamnatin jihar tana da hakki kan gudanar da harkokin kananan hukumomi, kuma abin da zai iya aiki a kai shi ne hanya mafi dacewa da za a ba da damar gudanar da ayyukan gwamnatin jihar, tare da gwamnoni da tsarin mulki ya tanadi hadin gwiwar asusun kananan hukumomi.

 

“Kudin tsarin mulki ya tanadar da shi ba gwamnatin tarayya ba ce ta tanadar da shi ba. Don haka a wane lokaci ya zama mara amfani?

 

“Haka kuma, ana ci gaba da tattauna wadannan batutuwa. A matsayinmu na jam’iyya, za mu yi ta tattaunawa a kai. Za mu kara tattaunawa da gwamnoninmu domin samun mafita.

 

“Na yi imanin cewa a karshe gwamnonin suna da rawar da za su taka dangane da gudanar da harkokin kananan hukumomi, saboda su suke da hakki fiye da kowa. Ina nufin dukkan alhakin gudanarwa, ba na tunanin za a kawo karshen wannan dambarwa.”

 

Mai magana da yawun jam’iyyar PDP ya ce damuwar jam’iyyar a fili take, domin kuwa kananan hukumomi suna da alaka da jihohi saboda sun fi kusa da juna.

 

“Yanzu a matsayinmu na jam’iyya, muna duba wannan hukuncin kotun koli a matsayin wani abun damuwa. Kuma zan fadi haka ne kasancewar gwamnatin tarayya na kokarin sake kirkiro wani tsarin mulkin kama-karya ko karkatar da al’amuran kananan hukumomi, muna ganin hakan zai zama wata hanyar kawo babbar matsala.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

'Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.