• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa duk da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomin, har yanzu da sauran rina a kaba.

 

Haka kuma babbar jam’iyyar adawar ta ce tana nazari kan martanin da suka biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke, tana mai cewa zai yi wuya a iya raba gwamnatin jiha da kananan hukumomi.

  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
  • Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa

Jam’iyyar ta bayyana matsayinta ne ta bakin sakataren yada labaranta na kasa, Honarabul Debo Ologunagba, yayin da yake jawabi ga manema labarai a shalkwatan jam’iyyar na kasa a ranar Lahadin da ta gabata.

 

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Da yake amsa tambaya kan matsayin Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, kan hukuncin kotun koli, Ologunagba ya ce, “Mun yi imanin cewa idan har za a yi wa kananan hukumomi garambawul, ya kamata a yi shi tare da gwamnoni ta yadda za su dace da bukatun gwamnatin tarayya.

 

“Tabbas, na yi imanin hakan ba zai kawo karshen lamarin ba, kamar yadda muke Magana saboda mutanen da ke da alhakkin kananan hukumomi su ne gwamnoni.

 

“Gwamnatin tarayya ba ta ganin mutane a kauyuka, gwamnoni ne suke yin hakan. Don haka idan akwai damuwa, to a hada kai da kananan hukumomi domin amfanar da al’umma, ba wai bukatar wasu ba.

 

“Doka ba ta nuni da abin da ba zai yiwu ba. Idan ta yi nuna da wani abu, za ta fadi hanyar warware duk wata matsala. Na tabbar da cewa mu ba mu ga cewa za a kawo karshen lamarin ba dangane da gudanar da kananan hukumomi.

 

“Gwamnatin jiha tana da alhakkin kan kananan hukumomi. Idan an samu matsala a kananan hukumomi, ba za su kira gwamnatin tarayya ba, za su kira gwamnatin jiha ne.

 

“Don haka dole ne a fahimci cewa gwamnatin jihar tana da hakki kan gudanar da harkokin kananan hukumomi, kuma abin da zai iya aiki a kai shi ne hanya mafi dacewa da za a ba da damar gudanar da ayyukan gwamnatin jihar, tare da gwamnoni da tsarin mulki ya tanadi hadin gwiwar asusun kananan hukumomi.

 

“Kudin tsarin mulki ya tanadar da shi ba gwamnatin tarayya ba ce ta tanadar da shi ba. Don haka a wane lokaci ya zama mara amfani?

 

“Haka kuma, ana ci gaba da tattauna wadannan batutuwa. A matsayinmu na jam’iyya, za mu yi ta tattaunawa a kai. Za mu kara tattaunawa da gwamnoninmu domin samun mafita.

 

“Na yi imanin cewa a karshe gwamnonin suna da rawar da za su taka dangane da gudanar da harkokin kananan hukumomi, saboda su suke da hakki fiye da kowa. Ina nufin dukkan alhakin gudanarwa, ba na tunanin za a kawo karshen wannan dambarwa.”

 

Mai magana da yawun jam’iyyar PDP ya ce damuwar jam’iyyar a fili take, domin kuwa kananan hukumomi suna da alaka da jihohi saboda sun fi kusa da juna.

 

“Yanzu a matsayinmu na jam’iyya, muna duba wannan hukuncin kotun koli a matsayin wani abun damuwa. Kuma zan fadi haka ne kasancewar gwamnatin tarayya na kokarin sake kirkiro wani tsarin mulkin kama-karya ko karkatar da al’amuran kananan hukumomi, muna ganin hakan zai zama wata hanyar kawo babbar matsala.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECSiyasaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

6 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

6 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

6 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

4 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

4 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 month ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

'Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.