ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa duk da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomin, har yanzu da sauran rina a kaba.

 

Haka kuma babbar jam’iyyar adawar ta ce tana nazari kan martanin da suka biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke, tana mai cewa zai yi wuya a iya raba gwamnatin jiha da kananan hukumomi.

ADVERTISEMENT
  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
  • Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa

Jam’iyyar ta bayyana matsayinta ne ta bakin sakataren yada labaranta na kasa, Honarabul Debo Ologunagba, yayin da yake jawabi ga manema labarai a shalkwatan jam’iyyar na kasa a ranar Lahadin da ta gabata.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Da yake amsa tambaya kan matsayin Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, kan hukuncin kotun koli, Ologunagba ya ce, “Mun yi imanin cewa idan har za a yi wa kananan hukumomi garambawul, ya kamata a yi shi tare da gwamnoni ta yadda za su dace da bukatun gwamnatin tarayya.

 

“Tabbas, na yi imanin hakan ba zai kawo karshen lamarin ba, kamar yadda muke Magana saboda mutanen da ke da alhakkin kananan hukumomi su ne gwamnoni.

 

“Gwamnatin tarayya ba ta ganin mutane a kauyuka, gwamnoni ne suke yin hakan. Don haka idan akwai damuwa, to a hada kai da kananan hukumomi domin amfanar da al’umma, ba wai bukatar wasu ba.

 

“Doka ba ta nuni da abin da ba zai yiwu ba. Idan ta yi nuna da wani abu, za ta fadi hanyar warware duk wata matsala. Na tabbar da cewa mu ba mu ga cewa za a kawo karshen lamarin ba dangane da gudanar da kananan hukumomi.

 

“Gwamnatin jiha tana da alhakkin kan kananan hukumomi. Idan an samu matsala a kananan hukumomi, ba za su kira gwamnatin tarayya ba, za su kira gwamnatin jiha ne.

 

“Don haka dole ne a fahimci cewa gwamnatin jihar tana da hakki kan gudanar da harkokin kananan hukumomi, kuma abin da zai iya aiki a kai shi ne hanya mafi dacewa da za a ba da damar gudanar da ayyukan gwamnatin jihar, tare da gwamnoni da tsarin mulki ya tanadi hadin gwiwar asusun kananan hukumomi.

 

“Kudin tsarin mulki ya tanadar da shi ba gwamnatin tarayya ba ce ta tanadar da shi ba. Don haka a wane lokaci ya zama mara amfani?

 

“Haka kuma, ana ci gaba da tattauna wadannan batutuwa. A matsayinmu na jam’iyya, za mu yi ta tattaunawa a kai. Za mu kara tattaunawa da gwamnoninmu domin samun mafita.

 

“Na yi imanin cewa a karshe gwamnonin suna da rawar da za su taka dangane da gudanar da harkokin kananan hukumomi, saboda su suke da hakki fiye da kowa. Ina nufin dukkan alhakin gudanarwa, ba na tunanin za a kawo karshen wannan dambarwa.”

 

Mai magana da yawun jam’iyyar PDP ya ce damuwar jam’iyyar a fili take, domin kuwa kananan hukumomi suna da alaka da jihohi saboda sun fi kusa da juna.

 

“Yanzu a matsayinmu na jam’iyya, muna duba wannan hukuncin kotun koli a matsayin wani abun damuwa. Kuma zan fadi haka ne kasancewar gwamnatin tarayya na kokarin sake kirkiro wani tsarin mulkin kama-karya ko karkatar da al’amuran kananan hukumomi, muna ganin hakan zai zama wata hanyar kawo babbar matsala.”

PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
PDP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

'Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.