• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen, Thomas Tuchel, ya bayyana cewa har yanzu wasa bai kare ba a haduwar su da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City a gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

A ranar Talata ne Manchester City ta doke Bayern Munich da ci 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a Champions League da suka kara ranar Talata a filin wasa na Etihad dake birnin Manchester.

  • Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Sallah: Gwamna Bagudu Ya Umarci A Biya Albashin Watan Afrilu

Minti 27 da fara wasa Manchester City ta ci kwallon ta hannun Rodrigo Hernandez, bayan da suka koma zagaye na biyu Bernardo Silba ya kara ta biyu, Erling Haaland ya ci ta uku minti bakwai tsakani.

Kuma kwallo ta 45 da Haaland ya ci a bana a dukkan fafatawa, ba wani dan wasan dake buga Premier mai wannan bajintar kuma wasa na bakwai da suka kara a Champions League a tsakaninsu, Manchester City ta ci hudu, Bayern ta yi nasara a uku.

”Duk da cewa mun yi rashin nasara hakan ba zai sanyaya mana gwiwa ba saboda akwai ragowar wasa nan gaba kuma naji na kara kaunar ‘yan wasa na saboda yadda suka buga wasa mai kyau.”

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Manchester City ta kawo wannan matakin bayan da ta fitar da RB Leipzig, ita kuwa Bayern ita ce ta yi waje da Paris St Germain, sannan wannan shi ne karon farko da suka kara a kuarter finals, bayan da sauran fafatawar da suka yi a cikin rukuni suka yi.

Wannan shi ne karo na 21 da Bayern ta kai wasan kusa da kusa da na karshe a kofin zakarun Turai, wadda ta dara Real Madrid mai 19 kuma Manchester City ce kadai cikin masu kai wa zagayen dab da na kusa da na karshe a kaka shida a jere a baya.

Wasa na karshe tsakanin Manchester City da Bayern shi ne na 2014, wanda kungiyar Ingila ta yi nasara a gida da cin 3-2 kuma kowacce ta ci uku-uku, wannan shi ne wasan farko da za su kece raini a zagayen kuarter finals, a cikin rukuni suka kara a baya a fafatawa shida.

Wasa shida tsakanin Man City da Bayern Munich

kofin zakarun Turai Talata 25 ga watan Nuwambar 2014. Man City 3 – 2 B kofin zakarun Turai Laraba 17 ga watan Satumbar 2014. B Munich 1 – 0 Man City. kofin zakarun Turai Tu 10Dec 2013. B Munich 2 – 3 Man City. kofin zakarun Turai 02Oct 2013. Man City 1 – 3 B Munich. kofin zakarun Turai 07Dec 2011. Man City 2 – 0 B Munich. Kofin Zakarun Turai Tu 27Sep 2011. B Munich 2 – 0 Man City. Bayern Munchen ta kai zagayen gaba a wasa biyar daga shida da ta fuskanci kungiyoyin Ingila a ziri daya kwalle, in ban da kakar 2018/19 a zagaye na biyu da Liberpool.

Bayern ta ci wasa hudu a jere a kan kungiyoyin Premier League, wasan farko da aka doke ta a karawa biyar da ta kai ziyara Ingila, wadda ta ci uku da canjaras daya. Sai dai Manchester City ta ci wasa na 11 a jere a gida a kan kungiyoyin Jamus a Champions League da cin kwallo 42 kuma aka zura mata guda 10.

Ranar Laraba 19 ga watan Afirilu, Bayern Munich za ta karbi bakuncin kungiyar Manchester City a wasa na biyu a Kofin Zakarun Turai zagayen kuarter finals a filin wasa na Allianz Arena.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bayern MunichMan CityTuchel
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gudu Zuwa Kasashen Waje: Gwamnati Na Shirin Taka Wa Likitoci Birki

Next Post

Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

5 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

7 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

7 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

1 week ago
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.