ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Tuchel

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen, Thomas Tuchel, ya bayyana cewa har yanzu wasa bai kare ba a haduwar su da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City a gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

A ranar Talata ne Manchester City ta doke Bayern Munich da ci 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a Champions League da suka kara ranar Talata a filin wasa na Etihad dake birnin Manchester.

  • Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Sallah: Gwamna Bagudu Ya Umarci A Biya Albashin Watan Afrilu

Minti 27 da fara wasa Manchester City ta ci kwallon ta hannun Rodrigo Hernandez, bayan da suka koma zagaye na biyu Bernardo Silba ya kara ta biyu, Erling Haaland ya ci ta uku minti bakwai tsakani.

ADVERTISEMENT

Kuma kwallo ta 45 da Haaland ya ci a bana a dukkan fafatawa, ba wani dan wasan dake buga Premier mai wannan bajintar kuma wasa na bakwai da suka kara a Champions League a tsakaninsu, Manchester City ta ci hudu, Bayern ta yi nasara a uku.

”Duk da cewa mun yi rashin nasara hakan ba zai sanyaya mana gwiwa ba saboda akwai ragowar wasa nan gaba kuma naji na kara kaunar ‘yan wasa na saboda yadda suka buga wasa mai kyau.”

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

Manchester City ta kawo wannan matakin bayan da ta fitar da RB Leipzig, ita kuwa Bayern ita ce ta yi waje da Paris St Germain, sannan wannan shi ne karon farko da suka kara a kuarter finals, bayan da sauran fafatawar da suka yi a cikin rukuni suka yi.

Wannan shi ne karo na 21 da Bayern ta kai wasan kusa da kusa da na karshe a kofin zakarun Turai, wadda ta dara Real Madrid mai 19 kuma Manchester City ce kadai cikin masu kai wa zagayen dab da na kusa da na karshe a kaka shida a jere a baya.

Wasa na karshe tsakanin Manchester City da Bayern shi ne na 2014, wanda kungiyar Ingila ta yi nasara a gida da cin 3-2 kuma kowacce ta ci uku-uku, wannan shi ne wasan farko da za su kece raini a zagayen kuarter finals, a cikin rukuni suka kara a baya a fafatawa shida.

Wasa shida tsakanin Man City da Bayern Munich

kofin zakarun Turai Talata 25 ga watan Nuwambar 2014. Man City 3 – 2 B kofin zakarun Turai Laraba 17 ga watan Satumbar 2014. B Munich 1 – 0 Man City. kofin zakarun Turai Tu 10Dec 2013. B Munich 2 – 3 Man City. kofin zakarun Turai 02Oct 2013. Man City 1 – 3 B Munich. kofin zakarun Turai 07Dec 2011. Man City 2 – 0 B Munich. Kofin Zakarun Turai Tu 27Sep 2011. B Munich 2 – 0 Man City. Bayern Munchen ta kai zagayen gaba a wasa biyar daga shida da ta fuskanci kungiyoyin Ingila a ziri daya kwalle, in ban da kakar 2018/19 a zagaye na biyu da Liberpool.

Bayern ta ci wasa hudu a jere a kan kungiyoyin Premier League, wasan farko da aka doke ta a karawa biyar da ta kai ziyara Ingila, wadda ta ci uku da canjaras daya. Sai dai Manchester City ta ci wasa na 11 a jere a gida a kan kungiyoyin Jamus a Champions League da cin kwallo 42 kuma aka zura mata guda 10.

Ranar Laraba 19 ga watan Afirilu, Bayern Munich za ta karbi bakuncin kungiyar Manchester City a wasa na biyu a Kofin Zakarun Turai zagayen kuarter finals a filin wasa na Allianz Arena.

Tuchel
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027
  • Abba Ibrahim Wada
    Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

MASU ALAKA

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman
Wasanni

NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

July 2, 2026
BUA Ya Musanta Rahoton Cewa Zai Sayi Kaso 70 Na Kano Pillars
Wasanni

BUA Ya Musanta Rahoton Cewa Zai Sayi Kaso 70 Na Kano Pillars

June 30, 2026
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.