ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Wasa Bai Kare Ba, Cewar Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Tuchel

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen, Thomas Tuchel, ya bayyana cewa har yanzu wasa bai kare ba a haduwar su da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City a gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

A ranar Talata ne Manchester City ta doke Bayern Munich da ci 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a Champions League da suka kara ranar Talata a filin wasa na Etihad dake birnin Manchester.

  • Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Sallah: Gwamna Bagudu Ya Umarci A Biya Albashin Watan Afrilu

Minti 27 da fara wasa Manchester City ta ci kwallon ta hannun Rodrigo Hernandez, bayan da suka koma zagaye na biyu Bernardo Silba ya kara ta biyu, Erling Haaland ya ci ta uku minti bakwai tsakani.

ADVERTISEMENT

Kuma kwallo ta 45 da Haaland ya ci a bana a dukkan fafatawa, ba wani dan wasan dake buga Premier mai wannan bajintar kuma wasa na bakwai da suka kara a Champions League a tsakaninsu, Manchester City ta ci hudu, Bayern ta yi nasara a uku.

”Duk da cewa mun yi rashin nasara hakan ba zai sanyaya mana gwiwa ba saboda akwai ragowar wasa nan gaba kuma naji na kara kaunar ‘yan wasa na saboda yadda suka buga wasa mai kyau.”

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Manchester City ta kawo wannan matakin bayan da ta fitar da RB Leipzig, ita kuwa Bayern ita ce ta yi waje da Paris St Germain, sannan wannan shi ne karon farko da suka kara a kuarter finals, bayan da sauran fafatawar da suka yi a cikin rukuni suka yi.

Wannan shi ne karo na 21 da Bayern ta kai wasan kusa da kusa da na karshe a kofin zakarun Turai, wadda ta dara Real Madrid mai 19 kuma Manchester City ce kadai cikin masu kai wa zagayen dab da na kusa da na karshe a kaka shida a jere a baya.

Wasa na karshe tsakanin Manchester City da Bayern shi ne na 2014, wanda kungiyar Ingila ta yi nasara a gida da cin 3-2 kuma kowacce ta ci uku-uku, wannan shi ne wasan farko da za su kece raini a zagayen kuarter finals, a cikin rukuni suka kara a baya a fafatawa shida.

Wasa shida tsakanin Man City da Bayern Munich

kofin zakarun Turai Talata 25 ga watan Nuwambar 2014. Man City 3 – 2 B kofin zakarun Turai Laraba 17 ga watan Satumbar 2014. B Munich 1 – 0 Man City. kofin zakarun Turai Tu 10Dec 2013. B Munich 2 – 3 Man City. kofin zakarun Turai 02Oct 2013. Man City 1 – 3 B Munich. kofin zakarun Turai 07Dec 2011. Man City 2 – 0 B Munich. Kofin Zakarun Turai Tu 27Sep 2011. B Munich 2 – 0 Man City. Bayern Munchen ta kai zagayen gaba a wasa biyar daga shida da ta fuskanci kungiyoyin Ingila a ziri daya kwalle, in ban da kakar 2018/19 a zagaye na biyu da Liberpool.

Bayern ta ci wasa hudu a jere a kan kungiyoyin Premier League, wasan farko da aka doke ta a karawa biyar da ta kai ziyara Ingila, wadda ta ci uku da canjaras daya. Sai dai Manchester City ta ci wasa na 11 a jere a gida a kan kungiyoyin Jamus a Champions League da cin kwallo 42 kuma aka zura mata guda 10.

Ranar Laraba 19 ga watan Afirilu, Bayern Munich za ta karbi bakuncin kungiyar Manchester City a wasa na biyu a Kofin Zakarun Turai zagayen kuarter finals a filin wasa na Allianz Arena.

Tuchel
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.