• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

by Sadiq
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aƙalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu a hare-haren ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

Ɗan majalisar jihar da ke wakiltar Malumfashi, Hon. Aminu Ibrahim, ya shaida wa majalisar dokokin jihar cewa ‘yan bindiga sun kashe mutane 30 da ke salla sannan suka ƙone mutane 20 da ransu a sabbin hare-haren da aka kai a ƙauyukan mazaɓarsa.

  • An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
  • Dole Ne Fasinjoji Su Kashe Wayoyinsu Gaba Ɗaya Kafin Jirgi Ya Tashi Ko Sauka – NCAA

Hare-haren sun faru ne a Gidan Adamu Mantau, Unguwar Yar Mai Dabo, Makera da kuma Burdigau.

Ibrahim ya ce lamarin ya bar jama’a cikin tsoro da baƙin ciki.

Ya bayyana cewa mazauna ƙauyukan sun yi kira da aka kai musu ɗauki kan hare-haren‘yan bindiga a kusa da Burdigau da misalin ƙarfe 6 zuwa 7 na yamma a ranar Litinin, amma sojoji sun iso daga baya suka kuma tafi ba tare da tsare yankin ba.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

Da safiyar ranar Talata, sai ‘yan bindiga suka kai farmaki Unguwar Mantau tare da buɗe wasu mutane da ke sallar Asubah wuta, inda suka kashe mutum 30.

“Lamarin ya zama abun baƙin ciki. Mutanenmu ba za su iya ci gaba da rayuwa a ƙauyukansu ba saboda waɗannan hare-hare marasa ƙarewa,” in ji Ibrahim, yana roƙon a kafa sansanonin sojoji a Karfi da Yaba.

Jawabin nasa ya tayar da hankali a tsakanin sauran ‘yan majalisa, waɗanda suka nuna cewa kisan gilla yana ƙaruwa a Katsina duk da ayyukan da sojoji ke yi a jihar.

Mazauna Malumfashi sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su ɗauki matakin gaggawa.

A baya an tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kashe masallata 13 ne a Unguwar Mantau da safiyar ranar Talata.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya shaida wa ‘yan jarida cewa gwamnati ta bayar da umarnin ƙara tsaro tare da kai wa waɗanda abin ya shafa tallafi.

“Lamarin ya faru ne lokacin da miyagu suka kai harin ramuwar gayya kan al’umma. Mutane na unguwar suna cikin masallaci suna sallar Asuba lokacin da miyagun suka fara harbe-harbe a cikin masallaci,” in ji Dr. Mu’azu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariKatsinaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

Next Post

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

Related

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

3 hours ago
majalisar kasa
Manyan Labarai

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

6 hours ago
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama
Manyan Labarai

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

21 hours ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

24 hours ago
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

1 day ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

1 day ago
Next Post
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al'adu Mai Taken "Sautin Zaman Lafiya" A Nairobi

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.