ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

by Sadiq
3 months ago
Katsina

Aƙalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu a hare-haren ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

Ɗan majalisar jihar da ke wakiltar Malumfashi, Hon. Aminu Ibrahim, ya shaida wa majalisar dokokin jihar cewa ‘yan bindiga sun kashe mutane 30 da ke salla sannan suka ƙone mutane 20 da ransu a sabbin hare-haren da aka kai a ƙauyukan mazaɓarsa.

  • An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
  • Dole Ne Fasinjoji Su Kashe Wayoyinsu Gaba Ɗaya Kafin Jirgi Ya Tashi Ko Sauka – NCAA

Hare-haren sun faru ne a Gidan Adamu Mantau, Unguwar Yar Mai Dabo, Makera da kuma Burdigau.

ADVERTISEMENT

Ibrahim ya ce lamarin ya bar jama’a cikin tsoro da baƙin ciki.

Ya bayyana cewa mazauna ƙauyukan sun yi kira da aka kai musu ɗauki kan hare-haren‘yan bindiga a kusa da Burdigau da misalin ƙarfe 6 zuwa 7 na yamma a ranar Litinin, amma sojoji sun iso daga baya suka kuma tafi ba tare da tsare yankin ba.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Da safiyar ranar Talata, sai ‘yan bindiga suka kai farmaki Unguwar Mantau tare da buɗe wasu mutane da ke sallar Asubah wuta, inda suka kashe mutum 30.

“Lamarin ya zama abun baƙin ciki. Mutanenmu ba za su iya ci gaba da rayuwa a ƙauyukansu ba saboda waɗannan hare-hare marasa ƙarewa,” in ji Ibrahim, yana roƙon a kafa sansanonin sojoji a Karfi da Yaba.

Jawabin nasa ya tayar da hankali a tsakanin sauran ‘yan majalisa, waɗanda suka nuna cewa kisan gilla yana ƙaruwa a Katsina duk da ayyukan da sojoji ke yi a jihar.

Mazauna Malumfashi sun roƙi gwamnatin jihar da ta tarayya da su ɗauki matakin gaggawa.

A baya an tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kashe masallata 13 ne a Unguwar Mantau da safiyar ranar Talata.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya shaida wa ‘yan jarida cewa gwamnati ta bayar da umarnin ƙara tsaro tare da kai wa waɗanda abin ya shafa tallafi.

“Lamarin ya faru ne lokacin da miyagu suka kai harin ramuwar gayya kan al’umma. Mutane na unguwar suna cikin masallaci suna sallar Asuba lokacin da miyagun suka fara harbe-harbe a cikin masallaci,” in ji Dr. Mu’azu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Nairobi

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al'adu Mai Taken "Sautin Zaman Lafiya" A Nairobi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.