• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Matafiya 18 Da Dabbobi Da Dama A Katsina

bySulaiman
9 months ago
Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

A wani lamari mai kayatarwa da jarumtaka, rundunar ‘yansandan jihar Katsina ta yi nasarar dakile hare-haren ‘yan bindiga guda biyu, tare da ceto matafiya mutane 18 da aka sace tare da kwato wasu dabbobi a wani hari kuma na daban.
Hare-haren da suka faru a ranar 3 ga Janairu, 2025, sun nuna irin kokarin da rundunar ‘yansandan Katsina ke yi na tabbatar da tsaro a fadin jihar.
  • NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa
  • Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota
A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, Sadiq Abubakar, ‘yan bindigar dauke da bindigogi kirar AK-47 sun yi wa wasu motoci hudu kwanton bauna kan hanyar Funtua zuwa Gusau, kan hanyar zuwa kauyen Yankara da wasu kuma Uku kuma sun fito daga Gusau.
Da yake amsa kiran gaggawa, shugaban rundunar ‘yansanda na Faskari (DPO) cikin gaggawa ya taso tawagarsa zuwa wurin.
Bayan artabu da ‘yan bindigar, jami’an sun tarwatsa ‘yan bindigar tare da ceto dukkan fasinjoji 18 ba tare da wani ya samu wani rauni ba.
Bugu da kari, Abubakar ya kara da cewa, a yammacin ranar da misalin karfe 11 na dare wasu ‘yan bindiga sun kuma sake kai wani hari kauyen Gidan Gada da ke karamar hukumar Kafur a jihar.
‘Yan Ta’addan sun tattaro shanu da dama tare da yin yunkurin tserewa da su.
A bisa bayanan sirri, tawagar jami’an hadin gwiwa daga Kafur da hedikwatar ‘yansanda ta Malumfashi sun bi sahun ‘yan ta’addan zuwa kauyen Fanisau.
Jami’an sun sake fafatawa da ‘yan bindigar, inda suka yi nasarar kwato dukkan dabbobin da suka sace.
Sai dai a yayin artabun, DPO na Kafur ya samu raunin harbin bindiga.
Nan take aka garzaya da shi asibiti, inda aka ce yana cikin koshin lafiya kuma yana karbar magani.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yabawa jami’an bisa jajircewarsu da kishinsu na ganin bayan ‘yan ta’adda a jihar.
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version