• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Matafiya 18 Da Dabbobi Da Dama A Katsina

by Sulaiman
10 months ago
Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

A wani lamari mai kayatarwa da jarumtaka, rundunar ‘yansandan jihar Katsina ta yi nasarar dakile hare-haren ‘yan bindiga guda biyu, tare da ceto matafiya mutane 18 da aka sace tare da kwato wasu dabbobi a wani hari kuma na daban.
Hare-haren da suka faru a ranar 3 ga Janairu, 2025, sun nuna irin kokarin da rundunar ‘yansandan Katsina ke yi na tabbatar da tsaro a fadin jihar.
  • NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa
  • Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota
A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, Sadiq Abubakar, ‘yan bindigar dauke da bindigogi kirar AK-47 sun yi wa wasu motoci hudu kwanton bauna kan hanyar Funtua zuwa Gusau, kan hanyar zuwa kauyen Yankara da wasu kuma Uku kuma sun fito daga Gusau.
Da yake amsa kiran gaggawa, shugaban rundunar ‘yansanda na Faskari (DPO) cikin gaggawa ya taso tawagarsa zuwa wurin.
Bayan artabu da ‘yan bindigar, jami’an sun tarwatsa ‘yan bindigar tare da ceto dukkan fasinjoji 18 ba tare da wani ya samu wani rauni ba.
Bugu da kari, Abubakar ya kara da cewa, a yammacin ranar da misalin karfe 11 na dare wasu ‘yan bindiga sun kuma sake kai wani hari kauyen Gidan Gada da ke karamar hukumar Kafur a jihar.
‘Yan Ta’addan sun tattaro shanu da dama tare da yin yunkurin tserewa da su.
A bisa bayanan sirri, tawagar jami’an hadin gwiwa daga Kafur da hedikwatar ‘yansanda ta Malumfashi sun bi sahun ‘yan ta’addan zuwa kauyen Fanisau.
Jami’an sun sake fafatawa da ‘yan bindigar, inda suka yi nasarar kwato dukkan dabbobin da suka sace.
Sai dai a yayin artabun, DPO na Kafur ya samu raunin harbin bindiga.
Nan take aka garzaya da shi asibiti, inda aka ce yana cikin koshin lafiya kuma yana karbar magani.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yabawa jami’an bisa jajircewarsu da kishinsu na ganin bayan ‘yan ta’adda a jihar.
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.