ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga: ‘Yansanda Sun Ceto Matafiya 18 Da Dabbobi Da Dama A Katsina

by Sulaiman
2 years ago
Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

A wani lamari mai kayatarwa da jarumtaka, rundunar ‘yansandan jihar Katsina ta yi nasarar dakile hare-haren ‘yan bindiga guda biyu, tare da ceto matafiya mutane 18 da aka sace tare da kwato wasu dabbobi a wani hari kuma na daban.
Hare-haren da suka faru a ranar 3 ga Janairu, 2025, sun nuna irin kokarin da rundunar ‘yansandan Katsina ke yi na tabbatar da tsaro a fadin jihar.
  • NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa
  • Sakataren Gwamnatin Ondo Ya Rasu Bayan Hatsarin Mota
A cewar kakakin rundunar ‘yansandan, Sadiq Abubakar, ‘yan bindigar dauke da bindigogi kirar AK-47 sun yi wa wasu motoci hudu kwanton bauna kan hanyar Funtua zuwa Gusau, kan hanyar zuwa kauyen Yankara da wasu kuma Uku kuma sun fito daga Gusau.
Da yake amsa kiran gaggawa, shugaban rundunar ‘yansanda na Faskari (DPO) cikin gaggawa ya taso tawagarsa zuwa wurin.
Bayan artabu da ‘yan bindigar, jami’an sun tarwatsa ‘yan bindigar tare da ceto dukkan fasinjoji 18 ba tare da wani ya samu wani rauni ba.
Bugu da kari, Abubakar ya kara da cewa, a yammacin ranar da misalin karfe 11 na dare wasu ‘yan bindiga sun kuma sake kai wani hari kauyen Gidan Gada da ke karamar hukumar Kafur a jihar.
‘Yan Ta’addan sun tattaro shanu da dama tare da yin yunkurin tserewa da su.
A bisa bayanan sirri, tawagar jami’an hadin gwiwa daga Kafur da hedikwatar ‘yansanda ta Malumfashi sun bi sahun ‘yan ta’addan zuwa kauyen Fanisau.
Jami’an sun sake fafatawa da ‘yan bindigar, inda suka yi nasarar kwato dukkan dabbobin da suka sace.
Sai dai a yayin artabun, DPO na Kafur ya samu raunin harbin bindiga.
Nan take aka garzaya da shi asibiti, inda aka ce yana cikin koshin lafiya kuma yana karbar magani.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yabawa jami’an bisa jajircewarsu da kishinsu na ganin bayan ‘yan ta’adda a jihar.
Yan Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.