• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashen Ambaliyar Ruwa A Kano: Wane Shiri Gwamnati Da Jama’ar Gari Suka Yi?

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Hasashen Ambaliyar Ruwa A Kano: Wane Shiri Gwamnati Da Jama’ar Gari Suka Yi?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hasashen yanayi na kwanan nan sun tayar da hankula game da yiwuwar ambaliyar ruwa a Jihar Kano. Hukumar lura da yanayi ta ƙasa (NiMet) ta yi hasashen cewa za a samu ruwan sama mai yawa a wasu jahohi da suka haɗa da Kano a watannin da ke tafe.

Wannan ƙaruwar ruwan sama, tare da matsalolin magudanun ruwa da gine-gine kan hanyoyin ruwa da Kano ke fuskanta, na ƙara haɗarin ambaliyar ruwa mai tsanani a yankunan birni da karkara. An shawarci mazauna waɗannan yankuna su kasance cikin shiri kuma su ɗauki matakan kariya don tsare rayuka da dukiyoyinsu.

Wani rahoton daga NiMeT ya bayyana cewa za a iya samu ambaliyar daga 16 zuwa 20 ga Yulin da muke ciki a ƙananan hukumomin:

  • Abba Ya Sake Nada Tsohon Sarkin Gaya Da Wasu Sabbin Sarakuna A Kano
  • Gobara Ta Yi Sanadin Mutuwar Iyalan Kwamishinan Ilimi A Kano

1-Gezawa

2-Gwarzo

Labarai Masu Nasaba

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

3-Karaye 

4-Wudil 

5-Sumaila

6- Cikin birni

Mahukunta sun fara ɗaukar wasu matakai na shirin rigakafi don rage illar wannan ambaliyar da ake tsammani. Waɗannan matakai sun haɗa da tsaftace magudanun ruwa, da gina katanga ta wucin gadi, da kuma wayar da kan jama’a game da shirin rigakafin ambaliyar ruwa.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kano (SEMA) tana aiki tare da shugabannin al’umma don tabbatar da cewa mazauna yankunan da ke cikin haɗari suna da cikakken bayani kuma sun shirya don yiwuwar kwashe su. Haka kuma, ƙungiyoyin ba da agajin gaggawa suna cikin shirin ko ta kwana don amsa kiran gaggawa da zarar an samu wani lamari.

Duk da wadannan shirye-shirye, akwai damuwa game da ƙarfin shirin jihar na magance ambaliyar ruwa mai tsanani, musamman idan aka yi la’akari da ƙalubalen da aka fuskanta a baya.

Masana na jan hankalin gwamnati da ta ƙara yin sabon tsarin da zai shigo da ma’aikatar tsara birane da ta kwashe shata da ƙungiyoyin matasa don rage haɗarin na dogon lokaci ba iya damunar bana ba.

An kuma jaddada buƙatar yin cikakken shiri wanda ya haɗa da tsarin gargadi na wuri-wuri kamar a Mota da majalisar Samari da wasu dabarun don gina ƙarfafawa mutane gwuiwa da juriya kan wasu manyan abubuwan da za su iya faru a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmbaliyaFloodkanoNiMetRuwaRuwan Sama
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Aike Wa Majalisa Takardar Neman Kara N6.2trn A Kasafin Kudin Bana

Next Post

Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa

Related

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

43 minutes ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

2 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

10 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

11 hours ago
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

13 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

14 hours ago
Next Post
Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa

Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba - Daliban Arewa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.