• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
IFAD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 4 ga watan Fabirairun 2025 ne, Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NiMet), ta kaddamar shirin hasashen yanayi na daminar noman bana (SCP).

Shirin, wanda hukumar ta kaddamar da a Abuja, wanda kundin hukumar da ta kaddamar ya nuna cewa, daukacin sassan kasar nan, za a samu ruwan sama mai yawan gaske, wanda kuma zai iya sauka tun kafin lokacin da ya kamata ya fara sauka.
Wani kwararre a fannin aikin noma, Cif Dennis Denen Gbongbon, ya sanar da cewa; akasarin manoma a yankin Arewa ta tsakiya, sun dogara ne ga saukar ruwan sama, wanda kuma za a iya samun jinkiri wajen saukarsa, inda ya ce, dole ne manoma su rika kula da tsarin sauyin lokaci.

  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka

Shi kuwa, wani kwararren a fannin ‘Teryima Iorlamen’, ya yi nuni da cewa, gyaran kasar noma da sauran saukar ruwan sama kafin a yi shuka, na da muhimmancin gaske ga manoma.

Hukumar ta yi hasashen cewa, jihohin Delta, Bayelsa, Ribas da Anambra da kuma wasu sassan Jihohin Oyo, Ogun, Osun, Ondo, Legas, Edo, Enugu, Imo da kuma Ebonyi, za su fara samun ruwan sama mai yawangaske.
Kazalika, hukumar ta yi hasashjen cewa; za a iya samun jinkirin ruwan sama a jihohi kamar irin su Filato, Kaduna, Neja, Biniwe, Nassarawa, Taraba, Adamawa da kuma Kwara.

Bugu da kari, a wasu sassan jihohi kamar su; Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Filato, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Taraba, Neja, Kwara, Kogi, Abuja, Ekiti da kuma Ondo, hukumar ta ce; ana sa ran samun saukar ruwan sama a farkon damina.
Sai dai, hasashen hukumar ya bayyana cewa; a wasu sassan Jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Legas, Kwara, Taraba, Oyo, Ogun, Kuros Riba, Delta, Akwa Ibom, Ebonyi, Anambra da kuma Enugu, za a iya samun jinkirin saukar ruwan saman a kakar noman ta bana.

Labarai Masu Nasaba

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Saboda haka ne, hukumar ta shawarci manoman da ke da ra’ayin noma a kakar noman ta bana da su tabbatar sun tuntube ta, ko kuma tuntubar sauran hukumomin da ke hasashen yanayi, domin sanin lokacin da ya ya fi dacewa su yi shuka.

Hukumar ta yi hasashen cewa, jihohin Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Filato, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Taraba, Neja, Kwara, Kogi, Abuja, Ekiti da kuma Ondo, za su fuskanci daukewar ruwan sama da wuri, inda aka kwatanta da na dogon zango da aka samu a daminar bara.
Haka zalika, hukumar ta yi hasashen cewa; za a samu jinkirin ruwan sama a wasu sasssan jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Legas, Kwara, Taraba, Oyo, Ogun, Kuros Riba, Delta, Akwa Ibom, Ebonyi, Anambra da kuma Enugu.

A cewar Hukumar, mai yiwuwa kakar daminar ta bana ta kasance gajera a wasu sassan Jihohin Borno da Yobe, sabanin yadda aka saba gani.

Hukumar ta yi hasashen cewa, mai yiwuwa kakar daminar ta bana, ta yi tsawo a Jihohin Legas da Nasarawa, sabanin yadda aka saba samu.

Hukumar ta yi hasashen cewa, daga watan Mayu zuwa na Yuni, za a samu ruwan sama kamar da baakin kwarya, wanda kuma mai yiwuwa, a samu afkuwar ambaliyar ruwa a wasu biranen da ke kusa da rafuka a kasar.
Kazalika, daga watan Afirilu zuwa na Mayu, yankunan Saki, Iseyin, Ogbomoso, Atisbo, Orelope, Itesiwaju, Olorunsgo, Kajola, Iwajowa da kuma Oro Ire da ke cikin Jihar Oyo, an yi hasashen samun karancin ruwan sama, wanda zai iya kai wa har tsawon kwana 15, bayan saukar ruwan saman.

Bugu da kari, Hukumar ta yi hasashen cewa; a wasu jihohin da ke Arewacin kasar nan, daga watan Yuni zuwa Yuli har zuwa watan Agustan 2025, za a samu karancin ruwan sama, wanda zai kai har tsawon kwana 21, inda kuma a Jihohin Ekiti, Osun, Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Anambra, Imo, Abia, Kuros Riba, Delta, Bayelsa da kuma Akwa Ibom, za a samu ruwan sama na tsaka-tsaki da zai kai kwana 15.

Daga tsakanin kwana 27 zuwa 40, za su shige ba tare da wani batun hasashe samun sauyin yanayi ba, haka za a fuskanci rani kadan a yankin Kudu Maso Gabas daga ranar 22 na 2025.

Saboda haka ne, kwararru a fannin aikin noma suka shawarci manoman kasar nan, musamman wadanda ke jihohin da ke tsakiyar kasar, da su tabbar da sun yi shuka da Irin da ke jurewa kowanne irin yanayi, musamman domin kauce wa fuskantar matsalar rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci a kakar noman ta 2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira

Next Post

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3)

Related

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

2 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

3 days ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Next Post
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3)

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.