• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira

by Hussein Yero
9 months ago
in Rahotonni
0
Hatsarin Kwalekwale A Zamfara: Asalin Abin Da Ya Faru Da Yadda Wasu Suka Tsira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar da ta gabata ne, jirgin kwale-kwale ya nitse da manoma a gwadaben bakin kasuwar da ke Karamar Hukumar Gummi ta Jihar Zamfara. 

An samu sabanin alkaluma na adadin wadanda suka rasa rayukansu; sakamakon taho mu gamu da kwale-kwalen ya yi da wani kwale-kwalen dauke da fasinjoji a ciki, wasu kafafen yada labarai sun bayyana cewa, sama da mutum 46 ne suka rasu.

  • Sin Ta Harba Tagwayen Taurarin Dan Adam Na Tsarin BeiDou
  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

Wannan dalili ne yasa, Fadar Shugaban Kasa da Ofishin Gwamnan Jihar Zamfara, suka fitar da sanarwar jaje tare da yin ta’aziya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da sauran al’ummar Zamfara da kasa baki-daya.

Guda daga cikin fasinjojin da tsira daga hatsarin da kwale-kwalen ya yi, Abubakar Danjuma; ya shaida wa wakilinmu yadda abin ya faru da kuma yadda Allah ya tseratar da shi, inda yake cewa; “Muna cikin kwale-kwalen, bayan mun kai tsakiyar ruwa; sai ga wani kwale-kwalen daga inda muka dosa ya kunno kai kawai ya bangaji namu kwale-kwalen; inda nan take igiyarsa ta katse.

Daga nan ne kuma, sai kawai kwale-kwalen namu ya fara tangal-tangal ruwa ya fara shiga ciki, sai ya rika yin kasa ruwa na ci gaba da shiga cikin nasa. Saboda haka, kafin zuwa wani dan lokaci; mun nitse a cikin ruwa, amma cikin ikon Allah da yake wasu daga cikinmu mun iya ruwa; sai Allah ya tseratar da rayukanmu, aka kuma samu nasarar ceto wasu daga ciki. Saboda haka, muna yi wa Allah godiya da ya kubutar da mu”, in ji Danjuma.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Shi kuwa, wanda ya rasa dansa; Malam Ibrahim ya bayyana cewa, haka Allah ya rubuta wa dana Muhammad cewa, a hadarin kwale-kwalen zai rasu; shi yasa ya amshi bawan nasa. Don haka, babu abin da zance da wuce Allah ya ji kansa tare da sauran wadanda suka rasu.

A nata banganen kuwa, Gwamnatin Jihar Zamfara; karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal, ta bai wa iyalan mamatan tallafin Naira miliyan ashirin.

Mataimakin Gwamnan Jihar, Malam Mani Mummuni ne ya bayyana haka, a lokacin ziyarar ta’aziya ga iyalan mamatan a Fadar Mai Martaba, Sarkin Mafaran Gummi, mai shari’a Hassan Lawal.

Mataimakin, ya kuma bayyana bakincikinsa ga iyalan wadanda suka rasu tare kuma da jajanta wa ‘yan’uwa da abokan arziki.

“Yanzu haka, mun bai wa kwamitin rabon tallafin agajin gaggawa wanda gwamnati ta kafa, karkashin jagorancin Alhaji Salihu mai buhu Gummi, wannan tallafi na Naira miliyan ashirin da za a raba wa iyalan wadanda iftila’in ya shafa.

“Haka zalika, gwamna yana tare da Shugabannin Hukumomin ba da agajin gaggawa da kuma hukumomin da abin ya shafa a kan matsalar madatsun ruwa, don gano matsalar da ke haifar da wadannan hadarurruka; domin kaucewa sake afkuwarsa a nan gaba,” in ji Mataimakin Gwamnan.

Haka zalika, Mataimakin Gwamnan; ya bayar da tabbacin cewa, dukkanin gwadaben da ake amfani da shi wajen tsallake ruwa, babu shakka gwamati za ta yi iya kokarinta na ganin ta samar da mafita.

Mai Martaba Sarkin Mafaran Gummi, Mai Shari’a Hassan Lawal; ya bayyana godiyarsa ga Gwamnatin Jihar Zamfara, kan ta’aziya da kuma tallafin kudi na Naira miliyan ashirin ga iyalan wadannan mamata.

Sarkin, ya kuma tabbatar da cewa; mutane goma ne kadai suka rasa rayukansu, ba arba’in ba kamar yadda wasu kafafen yada labarai suka bayyana. Kazalika, nan take ya bayyana sunayensu a gaban mahaifansu a cikin fadar tasa.

Sarkin Mafaran, ya kuma tabbatar wa da Mataimakin Gwamnan cewa; ya gayyato kungiyar masu kula da kwale-kwalen Jihar Kogi, don neman shawara a kan yadda za a magance matsalar asarar rayuka; sun kuma ba da tasu shawarar za kuma a mika zuwa ga gwamnati, domin shawo kan matsalar.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Gummi, Nuhu Falale ya bayyana cewa, kin bin doka ga shugabannin masu kulawa da kwale-kwalen, ke haifar da asarar rayukan al’umma.

A karshe, Falale ya yi kira ga gwamnatin jihar; ta taimaka wajen sama musu kwale-kwalen zamani, wanda za su rika amfani da shi wajen jigilar al’ummarsu, domin kaucewa asarar rayuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HatsariKwale-KwaleZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 

Next Post

Yunƙurin Sayar Da Jariri, Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 2 A Legas

Related

Hatsarin
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Yunƙurin Sayar Da Jariri, Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 2 A Legas

Yunƙurin Sayar Da Jariri, Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 2 A Legas

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Hatsarin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.