ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

by Sadiq
7 months ago
Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da ƙura bayan wallafa rubutu a shafinsa na sada zumunta kan cewar Amurka za ta ɗauki matakin soji a kan Nijeriya idan ba a daina kisan Kiristoci ba.

Waɗannan kalamai nasa sun tayar da hankalin jama’a, inda ma’aikatar tsaron Amurka ta fara nazarin wasu matakai don yiwuwar kai wa Nijeriya hari.

Masana Sun Ƙaryata Iƙirarin

Amma masana tsaro, lauyoyi, da masana diflomasoyi a Nijeriya da ƙasashen waje sun ce wannan magana tasa ba komai ba ce illa barazana da kuma siyasa, kuma ba zai iya ɗaukar kowane mataki a kan Nijeriya ba.

ADVERTISEMENT

Masana a Nijeriya sun yi watsi da ikirarin Trump da hujjojin da ya dogara da su. Bulama Bukarti, lauya kuma mai nazarin matsalar tsaro, ya ce batun “kisan Kiristoci” ba gaskiya ba ne amma iƙirarin na iya rura wutar ƙiyayya tsakanin addinai.

Ya bayyana cewa matsalar tsaro a Nijeriya ba ta addini ɗaya ba ce, domin ‘yan ta’adda suna kashe Musulmi da Kirista baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Dukkanin bayanan da ake da su sun nuna cewa babu wani kisan gillar da ake yi wa Kiristoci a Nijeriya… Wannan labarin ƙarya ne da ƙungiyoyi suka ƙirƙira, wanda Shugaba Trump ke ƙoƙarin yaɗawa.

“Wannan magana za ta iya ƙara tayar da hankali a Nijeriya… ‘Yan ta’adda suna kai hare-hare a kasuwanni, coci-coci, da masallatai, kuma suna kashe kowa ba tare da bambance tsakanin Musulmi da Kirista ba,” in ji Bukarti yayin wata hira da gidan talabijin na Al-Jazeera.

Masana da dama sun yi gargaɗin cewa irin wannan kalamai daga shugabanni na iya haddasa tashin hankali a ƙasar.

Martanin Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta kuma mayar da martani ta hanyar ƙaryata batun cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.

Ministan harkokin wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar, ya ce kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bai wa kowa damar yin addininsa cikin ‘yanci, don haka babu wani dalili da zai sa a ce gwamnati tana goyon bayan addini ɗaya.

Ya kuma ce Nijeriya na maraba da duk wani taimako da zai ƙara wa jami’an tsaronta ƙarfi wajen yaƙi da ta’addanci, amma cikin mutunta ƙasar.

Matakin Doka

A matakin doka kuwa, babu wata hanya da Amurka za ta iya kai wa Nijeriya hari kai-tsaye. Dokokin Majalisar Ɗinkin Duniya sun hana kowace ƙasa kai hari sai da izinin Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

Haka kuma, dokar Amurka ta ‘War Powers Act’ na buƙatar shugaban ƙasa ya sanar da majalisa cikin awa 48 idan zai tura sojoji ƙasar waje, kuma ya buƙaci amincewar majalisa idan za a tsawaita zaman sojojin.

Wannan na nufin cewa babu wata doka da za ta bai wa Trump damar kai hari kai-tsaye a Nijeriya.

A ɓangaren matakin soji kuwa, hakan ma ba abu ne mai sauƙi ba. Nijeriya tana da yawan jama’a sama da miliyan 220, tana da faɗin ƙasa da ke da wahalar sarrafawa, kuma rikice-rikicen da ake fuskanta a ƙasar sun samo asali ne daga ƙungiyoyin ‘yan ta’adda da na masu aikata laifuka.

Saboda haka, duk wani yunƙuri daga Amurka zai fi dacewa ya taƙaita ga bayar da horo, bayanan sirri, da tallafi wa sojojin Nujeriya, ba kai sojoji ƙasar ba.

Masana harkokin tsaro sun yi gargaɗin cewa irin wannan yunƙuri na iya haifar da tsadar abinci, asarar rayuka, da tashin hankali a ƙasar.

A yanzu dai, abin da zai iya yiwuwa shi ne amfani da hanyoyin diflomasiyya da takunkumi, maimakon yaƙi. Majalisar Dokoki ta Amurka na tattaunawa kan yiwuwar sanya wa mutanen da ke taimaka wa rikice-rikice a Nijeriya takunkumi, yayin da ECOWAS da sauran ƙasashen Afrika ke ƙaryata batun “yi wa Kiristoci kisan kiyashi”.

Masana a Nijeriya na jaddada cewa mafita game da lamarin shi ne haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da tsare-tsaren tsaro masu mutunta ikon ƙasar.

A gefe guda wasu na ganin ana so a yi amfani da bambacin addini ko siyasa domin samun damar yi wa Nijeriya kutse don samu damar wawushe mata albarkatun ƙasa kamar man fetur, ma’adanai da sauransu.

Wani lauya masanin harkokin tsaro mai suna Barista El-Zubair na ganin cewa akwai wasu ɓoyayyun dalilai da ya sa Trump ya fara waɗannan maganganu.

“Idan ya ce zai ɗauki matakin soji a kan Nijeriya, ta ina zai fara?

Nijeriya tana da girma da faɗi, kuma ga tarin al’umma, don haka wasu dalilai ne kawai suka saka yake waɗancan kalamai, amma batun ana kashe Kiristoci ba gaskiya ba ne, kawai yana son fakewa da shi ne don cimma wata manufa tasa.”

A taƙaice, dokokin ƙasa da ƙasa, ƙalubalen dabaru, da ra’ayoyin masana sun tabbatar da cewa kalaman Trump tsagwaron barazana ce ta siyasa, kuma ba gaske ba ce domin babu wata hujja da ta nuna ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.