ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

by Sadiq
10 months ago
Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da ƙura bayan wallafa rubutu a shafinsa na sada zumunta kan cewar Amurka za ta ɗauki matakin soji a kan Nijeriya idan ba a daina kisan Kiristoci ba.

Waɗannan kalamai nasa sun tayar da hankalin jama’a, inda ma’aikatar tsaron Amurka ta fara nazarin wasu matakai don yiwuwar kai wa Nijeriya hari.

Masana Sun Ƙaryata Iƙirarin

Amma masana tsaro, lauyoyi, da masana diflomasoyi a Nijeriya da ƙasashen waje sun ce wannan magana tasa ba komai ba ce illa barazana da kuma siyasa, kuma ba zai iya ɗaukar kowane mataki a kan Nijeriya ba.

ADVERTISEMENT

Masana a Nijeriya sun yi watsi da ikirarin Trump da hujjojin da ya dogara da su. Bulama Bukarti, lauya kuma mai nazarin matsalar tsaro, ya ce batun “kisan Kiristoci” ba gaskiya ba ne amma iƙirarin na iya rura wutar ƙiyayya tsakanin addinai.

Ya bayyana cewa matsalar tsaro a Nijeriya ba ta addini ɗaya ba ce, domin ‘yan ta’adda suna kashe Musulmi da Kirista baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Dukkanin bayanan da ake da su sun nuna cewa babu wani kisan gillar da ake yi wa Kiristoci a Nijeriya… Wannan labarin ƙarya ne da ƙungiyoyi suka ƙirƙira, wanda Shugaba Trump ke ƙoƙarin yaɗawa.

“Wannan magana za ta iya ƙara tayar da hankali a Nijeriya… ‘Yan ta’adda suna kai hare-hare a kasuwanni, coci-coci, da masallatai, kuma suna kashe kowa ba tare da bambance tsakanin Musulmi da Kirista ba,” in ji Bukarti yayin wata hira da gidan talabijin na Al-Jazeera.

Masana da dama sun yi gargaɗin cewa irin wannan kalamai daga shugabanni na iya haddasa tashin hankali a ƙasar.

Martanin Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta kuma mayar da martani ta hanyar ƙaryata batun cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.

Ministan harkokin wajen Nijeriya, Yusuf Tuggar, ya ce kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bai wa kowa damar yin addininsa cikin ‘yanci, don haka babu wani dalili da zai sa a ce gwamnati tana goyon bayan addini ɗaya.

Ya kuma ce Nijeriya na maraba da duk wani taimako da zai ƙara wa jami’an tsaronta ƙarfi wajen yaƙi da ta’addanci, amma cikin mutunta ƙasar.

Matakin Doka

A matakin doka kuwa, babu wata hanya da Amurka za ta iya kai wa Nijeriya hari kai-tsaye. Dokokin Majalisar Ɗinkin Duniya sun hana kowace ƙasa kai hari sai da izinin Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

Haka kuma, dokar Amurka ta ‘War Powers Act’ na buƙatar shugaban ƙasa ya sanar da majalisa cikin awa 48 idan zai tura sojoji ƙasar waje, kuma ya buƙaci amincewar majalisa idan za a tsawaita zaman sojojin.

Wannan na nufin cewa babu wata doka da za ta bai wa Trump damar kai hari kai-tsaye a Nijeriya.

A ɓangaren matakin soji kuwa, hakan ma ba abu ne mai sauƙi ba. Nijeriya tana da yawan jama’a sama da miliyan 220, tana da faɗin ƙasa da ke da wahalar sarrafawa, kuma rikice-rikicen da ake fuskanta a ƙasar sun samo asali ne daga ƙungiyoyin ‘yan ta’adda da na masu aikata laifuka.

Saboda haka, duk wani yunƙuri daga Amurka zai fi dacewa ya taƙaita ga bayar da horo, bayanan sirri, da tallafi wa sojojin Nujeriya, ba kai sojoji ƙasar ba.

Masana harkokin tsaro sun yi gargaɗin cewa irin wannan yunƙuri na iya haifar da tsadar abinci, asarar rayuka, da tashin hankali a ƙasar.

A yanzu dai, abin da zai iya yiwuwa shi ne amfani da hanyoyin diflomasiyya da takunkumi, maimakon yaƙi. Majalisar Dokoki ta Amurka na tattaunawa kan yiwuwar sanya wa mutanen da ke taimaka wa rikice-rikice a Nijeriya takunkumi, yayin da ECOWAS da sauran ƙasashen Afrika ke ƙaryata batun “yi wa Kiristoci kisan kiyashi”.

Masana a Nijeriya na jaddada cewa mafita game da lamarin shi ne haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da tsare-tsaren tsaro masu mutunta ikon ƙasar.

A gefe guda wasu na ganin ana so a yi amfani da bambacin addini ko siyasa domin samun damar yi wa Nijeriya kutse don samu damar wawushe mata albarkatun ƙasa kamar man fetur, ma’adanai da sauransu.

Wani lauya masanin harkokin tsaro mai suna Barista El-Zubair na ganin cewa akwai wasu ɓoyayyun dalilai da ya sa Trump ya fara waɗannan maganganu.

“Idan ya ce zai ɗauki matakin soji a kan Nijeriya, ta ina zai fara?

Nijeriya tana da girma da faɗi, kuma ga tarin al’umma, don haka wasu dalilai ne kawai suka saka yake waɗancan kalamai, amma batun ana kashe Kiristoci ba gaskiya ba ne, kawai yana son fakewa da shi ne don cimma wata manufa tasa.”

A taƙaice, dokokin ƙasa da ƙasa, ƙalubalen dabaru, da ra’ayoyin masana sun tabbatar da cewa kalaman Trump tsagwaron barazana ce ta siyasa, kuma ba gaske ba ce domin babu wata hujja da ta nuna ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.