• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

by Abdullahi Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kebbi, Alhaji Faruk Musa Yaro Enabo, ya bai wa Gwamna Nasir Idris da al’ummar Jihar tabbacin gudanar da aikin Hajji nagari.

Shugaban ya nuna matukar godiya ga Gwamna Idris bisa samun sa da ya cancanci a nada shi a irin wannan matsayi mai girma, inda ya yi alkawarin sauke dimbin amanar da aka dora masa.

  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi
  • Ku Yi Aiki Tukuru Ko Na Kore Ku, Tinubu Ga Ministoci

Shugaban hukumar ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar ragamar jagorancin hukumar a Birnin Kebbi, da kuma yin jawabi ga ma’aikatan hukumar da masu fatan alheri.

Shugaban ya gode wa Allah da ya ba shi wannan aiki na addini mai daraja, sannan ya sanya fata da amana, shi domin shiriya da taimako don sauke nauyin da ke kansa da matukar nasara.

Alhaji Faruk Musa ya bayyana sauran mambobin hukumar a matsayin fitattun mutane, inda ya ba da tabbacin cewa za su fara aiki nan take domin samun kyakkyawan aikin Hajji na aikin hajji mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Haka kuma ya yi bayanin tsarin bizar da kasar Saudiyya ta yi na aikin Hajjin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa, sabanin abin da aka samu a baya na wahalar da ake fuskanta na ba da biza cikin kankanin lokaci, bayar da bizar ga maniyyata daga yanzu zai dogara ne kan biyan kudin aikin Hajji gaba daya.

Sai dai ya bayyana cewa da zarar duk wani mahajjaci ya biya kudinsa gaba daya, hukumomin kasar Saudiyya za su ba shi bizar, inda ya ce tuni aka bude hanyar shiga ta kuma za a rufe bayan mako uku.

Shugaban ya sanar da duk mai niyyar zuwa aikin Hajji cewa makonni biyu kacal a cikinsu su biya kudin aikin Hajjin da ya kai Naira miliyan 4.5 sannan ya bukace su da su gaggauta biya.

Tun da farko, a jawabin maraba Alhaji Sani Idris Abarshi, sakataren hukumar ya bayyana farin cikinsa da nadin Faruq Musa Yaro Enabo a matsayin shugabanta, inda ya bayyana shi a matsayin wanda ya kware da kwazo.

Alhaji Sani Abarshi, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da Alhaji Faruk Musa wajen tafiyar da harkokin Hukumar Jin Dadin Alhazai, inda ya yi alkawarin ba shi dukkan goyon baya da hadin kai don samun nasara.

Cikin wadanda suka raka shugaban domin karbar ragamar mulki har da shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Muhammad Kana Zuru da dimbin masoya da abokan arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Na Sha Mugun Duka A Hannun ‘Yansanda — Ajaero

Next Post

Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

Related

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

1 hour ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

4 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

6 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

6 hours ago
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

7 hours ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

7 hours ago
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.