• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Zaɓen Kasar Laberiya Ta Karrama Shugaban INEC Da Lambar Yabo

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Hukumar Zaɓen Kasar Laberiya Ta Karrama Shugaban INEC Da Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Laberiya (NEC) ta yi jinjina da damƙa kambin yabo ga Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, bisa ƙoƙari da muhimmiyar rawar da ya taka wajen ƙara wa dimokuraɗiyya karsashi a Nijeriya.

Wannan karramawa ta fito ne daga Shugabar Hukumar Zaɓen Laberiya, Madam Davidetta Browne Lansanah, a ranar Juma’a, a Monrovia, babban birnin ƙasar.

  • Da Dumi-dumi: NAHCON Ta Kara Wa’adin Biyan Kujerar Aikin Hajjin 2024
  • Tudun Biri: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Kwamitin Sa Ido Kan Rabon Gudunmawa

An damƙa masa kambun girmamawar ne a wurin taron sanin makamar aiki da aka shirya wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya, wanda Farfesa Yakubu ya gajoranci horaswar.

A cikin jawabinta, Lansanah ta nuna farin ciki da gamsuwa da irin basira da kyawawan tsare-tsaren da INEC da Yakubu su ka shimfiɗa wa Hukumar Zaɓen Laberiya, wanda ta ce ya ƙara wa matakan shirya zaɓuɓɓukan ƙasar inganci da nagarta.

Ta nuna godiya ga Farfesa Yakubu, a madadin Hukumar Zaɓen Laberiya, bisa ga gagarumar rawar da ya taka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da matakan kafa dimokuraɗiyyar a Laberiya.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Da ta ke tuna rawar da gudunmawar da ya bayar a matsayinsa na Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Zaɓe na Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), Lansanah ta lissafo yadda ya tafiyar da ƙungiyar bisa nuna kishin aiki da bin ƙa’idoji. Ta kuma jinjina masa dangane da yadda ya riƙa ba ta goyon baya a matsayinta na Shugabar Hukumar Zaɓe ta Laberiya.

Farfesa

Da ya ke nuna godiya bisa karamcin da aka yi masa, Farfesa Yakubu ya bayyana farin ciki dangane da karramawar da Hukumar Zaɓen Laberiya ta yi wa INEC.

Haka kuma ya nuna muhimmancin nagartattun ayyuka da tsare-tsaren da ma’aikatan INEC su ka bijiro wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya.

Ya tuno da irin rawar da INEC ta bayar lokacin tsare-tsaren shirya zaɓen shugaban ƙasa a Laberiya da aka yi cikin 2017, sai kuma gudunmawar da INEC ɗin ta bayar a zaɓen raba-gardama cikin 2020, wanda ECOWAS ta gudanar.

Yakubu ya nuna yadda INEC ta taimaka wa hukumar zaɓen Laberiya wajen gina wa ƙasar turbar rajistar masu zaɓe ta hanyar tsarin na’urar tantance masu katin rajista.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASINECZaben kasar Laberiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 417 Da Dukiyoyin Nairori A Shekarar 2023

Next Post

Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

2 hours ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

4 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

5 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

6 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

18 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

19 hours ago
Next Post
Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.