• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Zaɓen Kasar Laberiya Ta Karrama Shugaban INEC Da Lambar Yabo

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Hukumar Zaɓen Kasar Laberiya Ta Karrama Shugaban INEC Da Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Laberiya (NEC) ta yi jinjina da damƙa kambin yabo ga Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, bisa ƙoƙari da muhimmiyar rawar da ya taka wajen ƙara wa dimokuraɗiyya karsashi a Nijeriya.

Wannan karramawa ta fito ne daga Shugabar Hukumar Zaɓen Laberiya, Madam Davidetta Browne Lansanah, a ranar Juma’a, a Monrovia, babban birnin ƙasar.

  • Da Dumi-dumi: NAHCON Ta Kara Wa’adin Biyan Kujerar Aikin Hajjin 2024
  • Tudun Biri: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Kwamitin Sa Ido Kan Rabon Gudunmawa

An damƙa masa kambun girmamawar ne a wurin taron sanin makamar aiki da aka shirya wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya, wanda Farfesa Yakubu ya gajoranci horaswar.

A cikin jawabinta, Lansanah ta nuna farin ciki da gamsuwa da irin basira da kyawawan tsare-tsaren da INEC da Yakubu su ka shimfiɗa wa Hukumar Zaɓen Laberiya, wanda ta ce ya ƙara wa matakan shirya zaɓuɓɓukan ƙasar inganci da nagarta.

Ta nuna godiya ga Farfesa Yakubu, a madadin Hukumar Zaɓen Laberiya, bisa ga gagarumar rawar da ya taka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da matakan kafa dimokuraɗiyyar a Laberiya.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Da ta ke tuna rawar da gudunmawar da ya bayar a matsayinsa na Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Zaɓe na Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), Lansanah ta lissafo yadda ya tafiyar da ƙungiyar bisa nuna kishin aiki da bin ƙa’idoji. Ta kuma jinjina masa dangane da yadda ya riƙa ba ta goyon baya a matsayinta na Shugabar Hukumar Zaɓe ta Laberiya.

Farfesa

Da ya ke nuna godiya bisa karamcin da aka yi masa, Farfesa Yakubu ya bayyana farin ciki dangane da karramawar da Hukumar Zaɓen Laberiya ta yi wa INEC.

Haka kuma ya nuna muhimmancin nagartattun ayyuka da tsare-tsaren da ma’aikatan INEC su ka bijiro wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya.

Ya tuno da irin rawar da INEC ta bayar lokacin tsare-tsaren shirya zaɓen shugaban ƙasa a Laberiya da aka yi cikin 2017, sai kuma gudunmawar da INEC ɗin ta bayar a zaɓen raba-gardama cikin 2020, wanda ECOWAS ta gudanar.

Yakubu ya nuna yadda INEC ta taimaka wa hukumar zaɓen Laberiya wajen gina wa ƙasar turbar rajistar masu zaɓe ta hanyar tsarin na’urar tantance masu katin rajista.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASINECZaben kasar Laberiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 417 Da Dukiyoyin Nairori A Shekarar 2023

Next Post

Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

6 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

6 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

7 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

9 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

11 hours ago
Next Post
Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.