ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Zaɓen Kasar Laberiya Ta Karrama Shugaban INEC Da Lambar Yabo

by Sulaiman
2 years ago
Laberiya

Hukumar Zaɓe ta Laberiya (NEC) ta yi jinjina da damƙa kambin yabo ga Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, bisa ƙoƙari da muhimmiyar rawar da ya taka wajen ƙara wa dimokuraɗiyya karsashi a Nijeriya.

Wannan karramawa ta fito ne daga Shugabar Hukumar Zaɓen Laberiya, Madam Davidetta Browne Lansanah, a ranar Juma’a, a Monrovia, babban birnin ƙasar.

  • Da Dumi-dumi: NAHCON Ta Kara Wa’adin Biyan Kujerar Aikin Hajjin 2024
  • Tudun Biri: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Kwamitin Sa Ido Kan Rabon Gudunmawa

An damƙa masa kambun girmamawar ne a wurin taron sanin makamar aiki da aka shirya wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya, wanda Farfesa Yakubu ya gajoranci horaswar.

ADVERTISEMENT

A cikin jawabinta, Lansanah ta nuna farin ciki da gamsuwa da irin basira da kyawawan tsare-tsaren da INEC da Yakubu su ka shimfiɗa wa Hukumar Zaɓen Laberiya, wanda ta ce ya ƙara wa matakan shirya zaɓuɓɓukan ƙasar inganci da nagarta.

Ta nuna godiya ga Farfesa Yakubu, a madadin Hukumar Zaɓen Laberiya, bisa ga gagarumar rawar da ya taka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da matakan kafa dimokuraɗiyyar a Laberiya.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Da ta ke tuna rawar da gudunmawar da ya bayar a matsayinsa na Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Zaɓe na Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), Lansanah ta lissafo yadda ya tafiyar da ƙungiyar bisa nuna kishin aiki da bin ƙa’idoji. Ta kuma jinjina masa dangane da yadda ya riƙa ba ta goyon baya a matsayinta na Shugabar Hukumar Zaɓe ta Laberiya.

Farfesa

Da ya ke nuna godiya bisa karamcin da aka yi masa, Farfesa Yakubu ya bayyana farin ciki dangane da karramawar da Hukumar Zaɓen Laberiya ta yi wa INEC.

Haka kuma ya nuna muhimmancin nagartattun ayyuka da tsare-tsaren da ma’aikatan INEC su ka bijiro wa ma’aikatan hukumar zaɓen Laberiya.

Ya tuno da irin rawar da INEC ta bayar lokacin tsare-tsaren shirya zaɓen shugaban ƙasa a Laberiya da aka yi cikin 2017, sai kuma gudunmawar da INEC ɗin ta bayar a zaɓen raba-gardama cikin 2020, wanda ECOWAS ta gudanar.

Yakubu ya nuna yadda INEC ta taimaka wa hukumar zaɓen Laberiya wajen gina wa ƙasar turbar rajistar masu zaɓe ta hanyar tsarin na’urar tantance masu katin rajista.

Laberiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

MASU ALAKA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027
Manyan Labarai

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato
Manyan Labarai

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina
Labarai

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Next Post
Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.