• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure

by Bello Hamza
11 months ago
in Kasashen Ketare, Labarai
0
Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga dukkan alamu hukumomin Saudiya sun samar da matakai na hana bakin haure da aka fi sani da Takari sakat a yayin gudanar da aikin hajjin bana na 2024.

Wakilinmu ya lura cewa, ‘yan Nijeriya maza da mata, wasu ma a kasar aka haifi iyayen su suna gudanar da harkokin saye da sayarwa na abinci da tufafi a kofofin Otal-otal da masallatan unguwannin da kuma hanyoyin zuwa masallacin Harami.

  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Ba NAHCON Izinin Buɗe Asibitoci Biyu A Kasar
  • Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah

A wannan shekarar bayan katin shaida na NSUK da aka bukaci kowanne Alhaji ya makala a wuya a yayin zirga zirgarsa a garin Makka domin gane Alhajin gaskiya da na bogi, Askarawa suna sintiri a kai a kai suna fattakar bakin hauren, “Za ka ga sun rungumi buhunan kayan da suke sayarwa suna gudu, abin gwanin ban tausayi”, in ji Alhaji Bello Bala Bungudu.

Hukumar kasar Saudiyya ta haramta wa duk wanda ba shi da izinin gudanar da aikin hajji shiga garin Makka ko da kuwa dan kasar ne, inda ta ayyana hukuncin daurin shekara 6 ga duk wanda aka kama da irin wannan laifin.

A tsokacinsa, wani dan jarida da ya dade yana shiga kasar Saudiya, Alhaji Kabir Yusuf, ya ce, yawancin irin wadannan mutanen suna shigowa ne da cikakken izini, ta hanyar zuwa Umara ko aikin Hajj ko kuma ta hannun kamfanonin daukar ma’aikata masu daukar ‘yan aikatau, amma da zaran takardar izinin zaman su ya kare sai su ci gaba da kulli kucciya tsakaninsu da jami’an tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Ya kara da cewa, a irin wannan ne zaka samu mutum ya yi shekaru a kasar, ya yi aure, ya hayayyafa, shida zuriyyarsa duk suna zama ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, duk da halin matsin tattalin arzikin da ake fuskanta a Nijeriya, ya kamata matasa su yi tunanin irin wulakancin da ake yi wa ‘yan Takari, “ Idan an kama mutum, bayan ya yi zaman gidan yari sai a kwace dukiyarsa a kuma fitar da shi zuwa wata kasar Afirka da karfin tsiya.
A kan haka ya shawarci gwamnati su farfado da tattalin azikin kasa ta yadda rayuwa zai yi dadi a Nijeriya.

Asibitocin NAHCON Sun Fara Aiki A Makkah
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da samun amincewar Ma’aikatar Lafiya ta Kasar Saudiya ta bude cibiyoyin lafiya guda biyu a garin Makkah domin aikin kula da lafiyar Alhazai a garin Makkah.

Ma’aikatar Lafiya ta kasar Saudiyya ta mika sakon ne ta hannun Kungiyar Kwararrun Likitocinta da ke aikin kula lafiya a karkashin kamfanin Ithra Alkhair, a cikin wata takardar da ta aike wa ofishin Hukumar NAHCON da ke birnin na Makkah. Tuni kuma suka fara aiki gadangadan.

Bayanin da ke kunshe a cikin takardar ya nuna cewa manyan asibitocin guda biyu wadanda za a bude za su kasance ne a unguwannin da ke Masfala/Kudai da yankin Shari’e Al-Mansour, za kuma su ci gaba da aiki a matsayin manyan asibitoci, za kuma su yi jinyar manya da kananan matsalolin lafiya da ka iya tasowa daga Alhazai a zaman su na Makkah.

Dakta Abubakar Adamu Isma’eel, Shugaban bangaren Ma’aikatan Lafiya na NAHCON masu aiki a a cikin garin Makkah a wannan shekarar (2024) ne ya karbi takardar amincewar a madadin hukumar Alhazai na Nijeriya.

A jawabinsa Dakta Abubakar ya bayyana cewa, a halin yanzu suna da karin wasu asibitoci uku da suke jiran a basu amincewar gudanar da aiki nan gaba kadan, wanda haka zai samu damar bayar da cikakkiyar kulawa ga dukkan Alhazan Nijeriya.

Asibitocin guda uku da za a bude a nan gaba za su samu cikakkiyar amincewar yin aiki kamar yadda ya kamata.

A ana sa ran asibitocin za su yi aiki ne a masaukan Alhazai guda uku da suka hada masaukan Alhazan Nasarawa, Ogun, Oyo da kuma Masaukan Alhazan Jihar Borno.

Ya kuma kara da cewa za a samar da na’urar GPS na wuraren da Assibitocin suke nan da dan lokaci domin al’umma su samun saukin gane asibitocin.

Tuni dai Hukumar NAHCON ta tura tawagar kwararrun likitocin da ke shirin aiki tukuru domin kulawa da lafiyar Alhazan Nijeriya. Don haka Hukumar ta nemi hadin kan Alhazan Nijeriya domin samun nasarar wannan aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HajjiSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Aniyar Amurka Ta Sayarwa Yankin Taiwan Makamai

Next Post

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

1 hour ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

3 hours ago
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

7 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

9 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

12 hours ago
Next Post
Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

LABARAI MASU NASABA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.