• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Zaben Nasarawa: PDP Za Ta Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Hukuncin Zaben Nasarawa: PDP Za Ta Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta bayyana rashin amincewarta game da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, na tabbatar da zaben Abdullahi Sule na jam’iyyar APC a jihar.

Tun da farko dai kotun sauraron kararrakin zabe ta ayyana dan takarar jam’iyyar PDP, Dr. David Ombugadu a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

  • Gaza: Isra’ila Ta Kashe Mutum 14,200, Daga Ciki Yara 6,000, Mata 4,000 – Jakadan Falasdin
  • Kotu Ta Bayar Da Belin Tsohon Shugaban Hukumar KASCO Kan Miliyan 500

Sai dai a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis mai dauke da sa hannun shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Hon. Francis Eokela Orogu, jam’iyyar adawa ta ce duk da cewa tana mutunta bangaren shari’a da bin doka, ta yi imani da cewa hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke bai yi daidai da hujjojin da aka gabatar a yayin zaman kotun ba.

Orogu ya ce, lauyoyin jam’iyyar sun gano wasu muhimman dalilai na daukaka kara wadanda suka yi imanin cewa ya kamata a sake duba hukuncin da kotun ta yanke.

Sanarwar ta kara da cewa: “Jam’iyyarmu za ta shigar da kara a gaban kotun kolin domin neman a yi mata adalci da kuma cikakken nazari kan hukuncin kotun daukaka kara, muna da kwarin gwiwa kan tsarin shari’a kuma muna da kwarin gwiwar cewa za a yi adalci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ya kara da cewa “gwagwarmayar tabbatar da adalci abu ne da ke bukatar juriya da hakuri, jam’iyyar PDP a Jihar Nasarawa ta jajirce wajen tabbatar da tsarin dimokuradiyya da tabbatar da adalci ga al’umma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuNasarawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gaza: Isra’ila Ta Kashe Mutum 14,200, Daga Ciki Yara 6,000, Mata 4,000 – Jakadan Falasdin

Next Post

Duniya Na Fatan Samun Karin Kadarori Masu Daraja Irin “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Related

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

50 minutes ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

3 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

7 hours ago
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
Manyan Labarai

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

8 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

17 hours ago
Next Post
Ziri Daya

Duniya Na Fatan Samun Karin Kadarori Masu Daraja Irin “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

July 3, 2025
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

July 3, 2025
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.