• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Kana da Kyau…

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Idan Kana da Kyau…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da al’ummar Sinawa a duk fadin duniya ke shirye-shiryen bikin bazara na wannan shekara, bikin gargajiya mafi kasaita ga al’ummar Sinawa, ko kuma bikin sabuwar shekara bisa kalandar gargajiyar kasar Sin, a hannu guda kuma hukumar kula da sufurin jiragen saman fasinjoji ta kasar Sin, ta ce wannan sashe na sa ran samun tafiye-tafiye miliyan 80 na fasinjoji yayin bikin sabuwar shekarar gargajiyar kasar dake tafe.

A cewar hukumar, wannan adadi ya kai karuwar kaso 44.9 idan aka kwatanta da makamancin lokacin a bara, kuma ya kai karuwar kaso 9.8 a kan wanda aka samu a makamancin lokaci na shekarar 2019.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Mai Sada Zumunta Ta Jihar Iowa Ta Amurka Sarah D. Lande
  • Yawan Kunshin Sakonni Da Aka Yi Jigilarsu A Kasar Sin Ya Kai Fiye Da Biliyan 160 A Shekarar 2023

Bayanai na nuna cewa, a bana tsawon lokacin tafiye-tafiyen zai kai har kusan kwanaki 40, wato daga ranar 26 ga watan Junairu zuwa 5 ga watan Maris.

A don haka, ana sa ran gudanar da a kalla tafiye-tafiye da bai gaza miliyan 2 ta jiragen sama ba a kullum, inda ake sa ran jirage da ba su gaza kimanin 16,500 za su rika tashi a kullum.

Domin biyan bukatun al’ummar kasar a fannin tafiye-tafiye yadda ya kamata, ita ma hukumar kula da jiragen kasa ta kasar ta bayyana cewa, za ta fara aiki da wani sabon shirin gudanar da layin dogo, daga ranar 10 ga watan Janairun shekarar 2024, da nufin inganta karfin jigilar kayayyaki da ma fasinjoji.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A karkashin sabon shirin, za a kara sabbin jiragen kasa na fasinja guda 233 a fadin kasar, wanda ya kawo jimillar adadinsu zuwa 11,149. Jimillar jiragen kasa na jigilar kayayyaki guda 22,264 ne za su rika aiki a fadin kasar, bayan shirin ya fara aiki, karuwar jirage 40, idan aka kwatanta da tsarin da ake amfani da shi a halin yanzu.

Wannan ya kara nuna cewa, duk da managartan hanyoyin sufuri na zamani da gwamnati ta samar a sassan kasar, a lokaci guda kuma, tana kokarin kara inganta su, ta yadda za su dace da zamani tare da biyan bukatun al’ummar kasar a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, matakan da ya dace kasashe su yi koyi da su, don sauke nauyin dake bisa wuyansu na bautawa jama’a. Wai idan kana da kyau to ka kara da wanka. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cigaban al’ummarsa sinJirgin KasaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Hisbah Ta Lalata Kwalaben Giya 850 A Katsina

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Satar Jariri A Nasarawa

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

16 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

16 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

23 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

24 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Satar Jariri A Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Satar Jariri A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Kyau

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.