• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Na Kalli ‘Certificates’ Da Na Samu Silar Rubutu Ina Jin Dadi Sosai – Fatima

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Fatima

A karkashen tattaunawar da marubuciya FATIMA SUNUSI RABI’U ta yi da shafin ADABI, ta bayyana irin nasarorin da ta samu a fannin rubutu, haka nan da kalubalen da abin ya kunsa kamar yadda PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU ta aiko mana kamar haka:

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdu lillah na samu nasarori sosai a silar rubutu, sanin ma mutane nasara ce. Domin silar rubutu na san mutane da dama a jahohi mabanbanta har ma da kasashen ketare ana zumunci da zama na amana. Haka a 2021 na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta daya a gasar Tambari Writers an karrama ni kuma an ba ni na kashewa. Haka na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta biyu a wata gasa ta Wiwan ita ma an karrama ni. A wannan shekarar kuma ta 2023 labarina ya zamo daya a cikin 13 a gasar Gusau Institute an ba ni Certificate, sannan akwai kananun alkhairai sosai da na cimma nasara duk a silar rubutu.

 

Me za ki ce da masu karanta littattafanki?

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Tsakani na da masu karatu sai sam-barka akwai amana sosai, sai dai na yi musu fatan alkhairi. Kalubale bai wuce na wasu da kake dangantaka da su ba ka ji ana ce maka, baka da aikin yi, rubutu ai wahalar da kai ne, koma a yi maka kallon kamar ba ka san me kake ba. Sauran kalubale kam ba na kallonsu da yazo idan ya wuce nake manta komi.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Kowa yana da buri a rayuwarsa wasu su cika wasu kuma har ka rasu da burinka, ina fatan Allah ya cika mini burikana na alkhairi, wasu daga ciki, ina fatan na yi rubutun da zai zaga ko ina a duniya na shiga cikin wadanda za a dinga kwatance da su kuma yin alfahari da rubutunsu. Sannan ina da burin ganin na bude wata gidauniya domin taimakon marayu da mabukata.

 

Wanne irin yabo ki ke samu wajen masu karanta labaranki?

Yabawa ta nawa kuwa, gaskiya ina samun mutane da ke yabawa wasu har kira a waya a yaba maka. Bata rai bai wuce na idan kana littafin kudi ba ka dan sami wani akasin da baka yi rubutu ba ka ji ana ta magana musamman ta ‘pribate’ cewa ka amshi kudi amma shuru babu ‘posting’. Wani lokacin dole ne take sa a ji ka shuru kwana biyu, amma kuma da zarar ka ci gaba sai komi ya wuce.

 

Wanne abu ne idan ki ka tuna shi yake saka ki farin ciki?

Idan na kalli ‘Certificates’ dina wadanda silar rubutu na same su, ina jin dadi sosai.

 

Bayan rubutu kina sana’a?

Eh! ina sana’a kam, ko ince sana’o’i ma. AlhamduLillah.

 

Ya ki ke iya hada sana’arki da kuma rubutu?

[Dariya] komai da lokacinsa, sannan gaskiya ni yanzu na tsara yadda nake rubutuna ba kamar baya ba, muna da kungiya ta gwawurtattu uku to mun tsara a duk shekara zamu fitar da labarai guda biyu ne, don haka komai yana da lokacinsa.

 

Kamar wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

To idan har ina da lokaci kuma ina jin yin rubutun to ina iya yi, kawai dai na fi son yanayin da zan tsince ni shuru babu hayaniya, ina yawan yin rubutu bayan sallar isha’i, dana yi sai na kwanta na yi bacci.

 

Me za ki ce da masu karanta littafinki?

Ina kaunarsu a kowanne lokaci, kuma ina musu fatan alkhairi sannan ina fatan su ci gaba da bina a duk lokacin da na saki sabon littafi. Ina kaunarsu kamar yadda suke kaunata da littattafaina.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

To ma sha Allahu, ina gaida kanwata Dr Maryamah Ibrahim marubuciya da aminyata Rukayya Ibrahim Lawal sai gawurtattu uku Badi’at Mrs Bukhari da Ummu Maheer Miss Green sannan ina gaishe da Auntyna Hadiza Ibrahim D Auta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.