ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Na Kalli ‘Certificates’ Da Na Samu Silar Rubutu Ina Jin Dadi Sosai – Fatima

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Fatima

A karkashen tattaunawar da marubuciya FATIMA SUNUSI RABI’U ta yi da shafin ADABI, ta bayyana irin nasarorin da ta samu a fannin rubutu, haka nan da kalubalen da abin ya kunsa kamar yadda PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU ta aiko mana kamar haka:

Wanne irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdu lillah na samu nasarori sosai a silar rubutu, sanin ma mutane nasara ce. Domin silar rubutu na san mutane da dama a jahohi mabanbanta har ma da kasashen ketare ana zumunci da zama na amana. Haka a 2021 na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta daya a gasar Tambari Writers an karrama ni kuma an ba ni na kashewa. Haka na samu nasarar zuwa gwarzuwa ta biyu a wata gasa ta Wiwan ita ma an karrama ni. A wannan shekarar kuma ta 2023 labarina ya zamo daya a cikin 13 a gasar Gusau Institute an ba ni Certificate, sannan akwai kananun alkhairai sosai da na cimma nasara duk a silar rubutu.

ADVERTISEMENT

 

Me za ki ce da masu karanta littattafanki?

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Tsakani na da masu karatu sai sam-barka akwai amana sosai, sai dai na yi musu fatan alkhairi. Kalubale bai wuce na wasu da kake dangantaka da su ba ka ji ana ce maka, baka da aikin yi, rubutu ai wahalar da kai ne, koma a yi maka kallon kamar ba ka san me kake ba. Sauran kalubale kam ba na kallonsu da yazo idan ya wuce nake manta komi.

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Kowa yana da buri a rayuwarsa wasu su cika wasu kuma har ka rasu da burinka, ina fatan Allah ya cika mini burikana na alkhairi, wasu daga ciki, ina fatan na yi rubutun da zai zaga ko ina a duniya na shiga cikin wadanda za a dinga kwatance da su kuma yin alfahari da rubutunsu. Sannan ina da burin ganin na bude wata gidauniya domin taimakon marayu da mabukata.

 

Wanne irin yabo ki ke samu wajen masu karanta labaranki?

Yabawa ta nawa kuwa, gaskiya ina samun mutane da ke yabawa wasu har kira a waya a yaba maka. Bata rai bai wuce na idan kana littafin kudi ba ka dan sami wani akasin da baka yi rubutu ba ka ji ana ta magana musamman ta ‘pribate’ cewa ka amshi kudi amma shuru babu ‘posting’. Wani lokacin dole ne take sa a ji ka shuru kwana biyu, amma kuma da zarar ka ci gaba sai komi ya wuce.

 

Wanne abu ne idan ki ka tuna shi yake saka ki farin ciki?

Idan na kalli ‘Certificates’ dina wadanda silar rubutu na same su, ina jin dadi sosai.

 

Bayan rubutu kina sana’a?

Eh! ina sana’a kam, ko ince sana’o’i ma. AlhamduLillah.

 

Ya ki ke iya hada sana’arki da kuma rubutu?

[Dariya] komai da lokacinsa, sannan gaskiya ni yanzu na tsara yadda nake rubutuna ba kamar baya ba, muna da kungiya ta gwawurtattu uku to mun tsara a duk shekara zamu fitar da labarai guda biyu ne, don haka komai yana da lokacinsa.

 

Kamar wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

To idan har ina da lokaci kuma ina jin yin rubutun to ina iya yi, kawai dai na fi son yanayin da zan tsince ni shuru babu hayaniya, ina yawan yin rubutu bayan sallar isha’i, dana yi sai na kwanta na yi bacci.

 

Me za ki ce da masu karanta littafinki?

Ina kaunarsu a kowanne lokaci, kuma ina musu fatan alkhairi sannan ina fatan su ci gaba da bina a duk lokacin da na saki sabon littafi. Ina kaunarsu kamar yadda suke kaunata da littattafaina.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

To ma sha Allahu, ina gaida kanwata Dr Maryamah Ibrahim marubuciya da aminyata Rukayya Ibrahim Lawal sai gawurtattu uku Badi’at Mrs Bukhari da Ummu Maheer Miss Green sannan ina gaishe da Auntyna Hadiza Ibrahim D Auta.

Fatima
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

Li Qiang Ya Tattauna Da Kwararrun ‘Yan Kasashen Waje Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.