• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illolin Rashin Yawan Shan Ruwa Ga Dan’Adam

by Sani Anwar
2 years ago
in Kiwon Lafiya
0
Illolin Rashin Yawan Shan Ruwa Ga Dan’Adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yadda Allah (SWT) ya halicci Dan Adam, kaso 60 cikin 100 na jikin namiji ruwa ne zalla, inda mata kuma kaso 55 na jikinsu su ma ruwa.

Don haka, wannan yana nuna cewa fiye da rabin jikin Dan Adam ruwa ne, saboda haka da zarar an ce babu wannan ruwan tare da mu, kenan babu rai kwata-kwata.

  • Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Kama Hanyar Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba A Yankin Tsaunin Himalaya
  • Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Har ila yau, shan ruwa na da matukar amfani a tare da mutane, domin kuwa a kullum ruwa na fita daga jikinmu, idan muka je yin fitsari ko bayan gida ko yin zufa, kai har ma yayin da muke yin numfashi.

Kazalika, ana bukatar da namiji ya sha ruwa kimanin lita 3.7, mata kuma su sha lita 2.7 a kowace rana. A nan ana auna yawan ruwan da mutum ke sha ne wanda ya hada da shayi ko lemo ko kuma jus.

Idan kuma zallan ruwan mutum zai sha kamar ‘Pure Water’, namiji ana so ya sha kamar guda bakwai da rabi, mace kuma ta sha guda biyar da rabi.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Amma a nan ana magana ne a kan lafiyayyu, wadanda ba su da cikakkiyar lafiya kamar masu ciwon zuciya ko koda, bai kamata su sha wannan adadi ba.

Rashin yawan shan ruwa yadda ya kamata zai iya jawo wa mutum illoli daban daban. Na farko, rashin shan ruwa akai-akai zai iya haddasa wa mutum ya kamu da cutar sanyin fitsari (Urinary track infection).

Na biyu kuma, zai iya haddasa wa mutum cutar tsakuwar koda (Kidney stones), a nan wasu abubuwa ne ke dunkulewa su ki fita su zama kamar dutse, wanda hakan ke sa wa mutum ya rika yin ciwon ciki mai zafi tare da yin fitsarin jini da sauran wasu matsaloli da dama.

Na uku kuma, rashin yawan shan ruwa na iya janyo rashin iya yin bayan gida, wanda hakan kan kawo matsalar basir da sauran makamantansu sakamakon sakaci da yawan shan ruwa.

Don haka, ya zama wajibi mu kula da shan shan ruwa yadda ya kamata, domin kaucewa haduwa da ire-iren wadannan cututtuka, kamar yadda a koda-yaushe likitoci ke kokarin fadakarwa tare da jan hankalinmu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

“Makon Zinare” Ya Kore Surutan Tabarbarewar Tattalin Arzikin Kasar Sin 

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Related

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

1 week ago
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi
Kiwon Lafiya

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

1 week ago
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Kiwon Lafiya

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

2 weeks ago
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
Kiwon Lafiya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

1 month ago
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
Kiwon Lafiya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

1 month ago
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
Kiwon Lafiya

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

2 months ago
Next Post
Uba sani

Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.