ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Jks

“Zan so in koma gida ba tare da bata lokaci ba, don in gabatar da dabarun ga abokanan aikina”. A watan Afrilun bana, tawagar wakilan jam’iyyar UDA mai mulki ta kasar Kenya ta kawo ziyara kasar Sin a karkashin jagorancin babban sakatarenta Mr. Hassan Omar, kuma dabarun jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na gudanar da harkokinta sun burge su matuka. A cewar Mr. Omar, kasar Sin tana da kwarewa da dabarun saukaka fatara da tabbatar da adalci ga al’umma, wadanda suke iya zama abin koyi ga Kenya a kokarinta na aiwatar da gyare-gyare ga tattalin arziki da zaman al’umma da kuma siyasa. 

A ganin mambobin tawagar Kenya, idan ana son fahimtar dalilin ci gaban kasar Sin, dole ne a fara da fahimtar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tukuna, kuma wannan ra’ayi yana ta kara samun karbuwa a tsakanin karin ‘yan siyasa da kwararrun masana na kasashe daban daban. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin jam’iyya ce mai mulki a kasar, wadda aka kafa ta a shekarar 1921, kuma kawo yanzu shekarunta sun kai 104. Me ya sa jam’iyyar mai tsawon tarihi na sama da shekaru 100 har yanzu take dorewa a kan mulki? A ganina, babban dalili shi ne yadda jam’iyyar take daukar jama’a a matsayin tushen ayyukan da take sanyawa a gaba. A shekaru 80 da suka wuce, an taba yi wa tsohon jagoran jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin marigayi Mao Zedong tambaya cewa, ta yaya jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin zata iya dorewa? Ya amsa da cewa, “A bar jama’a su sa ido a kan aikin gwamnati”. Sai kuma da muka shiga sabon zamani, jam’iyyar ta gano sabuwar mafita, wato a dinga yi wa jam’iyyar kwaskwarima. Kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce, “Kasa ita ce jama’a, kuma jama’a su ne kasa. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’a su kafa kasarsu da kiyaye ta, domin kiyaye imanin jama’a a kan ta.” Lallai bauta wa jama’a bisa iya kokarinta, shi yake samar wa jam’iyyar kwarin gwiwa da niyyar yi wa kanta kwaskwarima, haka kuma shi ne ainihin dalilin da ya sa take samun goyon baya daga jama’a.

  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

“Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana samun farin jini wurin jama’a, wannan kuma shi ne sirrin nasarorin da ta samu. Manufar gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya da ta gabatar ma tana shafar jama’a. Aminaina Sinawa su kan ce ‘kada mu manta da ainihin abin da muke neman cimmawa’, to, a ganina wannan shi ne abin da ake neman cimmawa”, in ji Jose Julio Gomez Beato, jakadan kasar Dominica a kasar Sin. Abin hakan yake, tun farkon kafuwarta, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta mai da samar wa al’umma alheri da kuma farfado da al’ummar Sinawa a matsayin ainihin abin da take neman cimmawa. Sai dai ba kamar jam’iyyun siyasa na wasu kasashe da su kan jaddada sanya kasashensu a gaba da kome ba, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin a nata bangare tana kokarin amfanar al’ummar kasar, tana kuma kokartawa don tabbatar da ganin ci gaban dan Adam baki daya, wannan kuma shi ne dalilin da ya sa ta gabatar da manufarta ta “gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya”.

ADVERTISEMENT

Alkaluman da aka samar a ranar 30 ga watan Yunin da ya gabata sun nuna cewa, kawo karshen bara, yawan ‘yan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya zarce miliyan 100, kuma yawan wadanda suka mika rokonsu na zama ‘ya‘yan jam’iyyar ya wuce miliyan 20, alkaluman da kuma suka shaida jam’iyyar na matukar samun karbuwa a tsakanin al’ummar kasar.

Tun bayan kafuwarta shekaru 104 da suka gabata, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’ar kasar wajen samun nasarar juyin juya hali a kasar, daga nan kuma, ta jagoranci jama’ar kasar wajen tabbatar da saurin bunkasar tattalin arziki da al’umma mai zaman lumana a kasar, nasarorin da suka kasance na a zo a gani a duniya. Sabo da jama’a take kokartawa, kuma ta dogara da jama’a wajen cimma nasara.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

‘Yan tawagar jam’iyyar UDA ta kasar Kenya da suka kawo ziyara kasar Sin sun kwatanta jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da bishiyar kuka, suna cewa, “Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tamkar bishiyar kuka ce, wadda ke da ingantattun saiwoyi da ma babban karfi na warkar da kanta, tana ta fid da furanni da ‘ya’ya ba tare da tsayawa ba” “bishiyoyin kuka suna da tsawon rai na sama da shekaru dubu”. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana cikin karfinta, kuma za ta ci gaba da kokartawa domin bauta wa jama’a, tare da dogara da jama’a don cimma karin nasarori.

 

Jks
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Jks
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.