ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Jks

“Zan so in koma gida ba tare da bata lokaci ba, don in gabatar da dabarun ga abokanan aikina”. A watan Afrilun bana, tawagar wakilan jam’iyyar UDA mai mulki ta kasar Kenya ta kawo ziyara kasar Sin a karkashin jagorancin babban sakatarenta Mr. Hassan Omar, kuma dabarun jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na gudanar da harkokinta sun burge su matuka. A cewar Mr. Omar, kasar Sin tana da kwarewa da dabarun saukaka fatara da tabbatar da adalci ga al’umma, wadanda suke iya zama abin koyi ga Kenya a kokarinta na aiwatar da gyare-gyare ga tattalin arziki da zaman al’umma da kuma siyasa. 

A ganin mambobin tawagar Kenya, idan ana son fahimtar dalilin ci gaban kasar Sin, dole ne a fara da fahimtar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tukuna, kuma wannan ra’ayi yana ta kara samun karbuwa a tsakanin karin ‘yan siyasa da kwararrun masana na kasashe daban daban. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin jam’iyya ce mai mulki a kasar, wadda aka kafa ta a shekarar 1921, kuma kawo yanzu shekarunta sun kai 104. Me ya sa jam’iyyar mai tsawon tarihi na sama da shekaru 100 har yanzu take dorewa a kan mulki? A ganina, babban dalili shi ne yadda jam’iyyar take daukar jama’a a matsayin tushen ayyukan da take sanyawa a gaba. A shekaru 80 da suka wuce, an taba yi wa tsohon jagoran jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin marigayi Mao Zedong tambaya cewa, ta yaya jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin zata iya dorewa? Ya amsa da cewa, “A bar jama’a su sa ido a kan aikin gwamnati”. Sai kuma da muka shiga sabon zamani, jam’iyyar ta gano sabuwar mafita, wato a dinga yi wa jam’iyyar kwaskwarima. Kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce, “Kasa ita ce jama’a, kuma jama’a su ne kasa. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’a su kafa kasarsu da kiyaye ta, domin kiyaye imanin jama’a a kan ta.” Lallai bauta wa jama’a bisa iya kokarinta, shi yake samar wa jam’iyyar kwarin gwiwa da niyyar yi wa kanta kwaskwarima, haka kuma shi ne ainihin dalilin da ya sa take samun goyon baya daga jama’a.

  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

“Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana samun farin jini wurin jama’a, wannan kuma shi ne sirrin nasarorin da ta samu. Manufar gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya da ta gabatar ma tana shafar jama’a. Aminaina Sinawa su kan ce ‘kada mu manta da ainihin abin da muke neman cimmawa’, to, a ganina wannan shi ne abin da ake neman cimmawa”, in ji Jose Julio Gomez Beato, jakadan kasar Dominica a kasar Sin. Abin hakan yake, tun farkon kafuwarta, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta mai da samar wa al’umma alheri da kuma farfado da al’ummar Sinawa a matsayin ainihin abin da take neman cimmawa. Sai dai ba kamar jam’iyyun siyasa na wasu kasashe da su kan jaddada sanya kasashensu a gaba da kome ba, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin a nata bangare tana kokarin amfanar al’ummar kasar, tana kuma kokartawa don tabbatar da ganin ci gaban dan Adam baki daya, wannan kuma shi ne dalilin da ya sa ta gabatar da manufarta ta “gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya”.

ADVERTISEMENT

Alkaluman da aka samar a ranar 30 ga watan Yunin da ya gabata sun nuna cewa, kawo karshen bara, yawan ‘yan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya zarce miliyan 100, kuma yawan wadanda suka mika rokonsu na zama ‘ya‘yan jam’iyyar ya wuce miliyan 20, alkaluman da kuma suka shaida jam’iyyar na matukar samun karbuwa a tsakanin al’ummar kasar.

Tun bayan kafuwarta shekaru 104 da suka gabata, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’ar kasar wajen samun nasarar juyin juya hali a kasar, daga nan kuma, ta jagoranci jama’ar kasar wajen tabbatar da saurin bunkasar tattalin arziki da al’umma mai zaman lumana a kasar, nasarorin da suka kasance na a zo a gani a duniya. Sabo da jama’a take kokartawa, kuma ta dogara da jama’a wajen cimma nasara.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

‘Yan tawagar jam’iyyar UDA ta kasar Kenya da suka kawo ziyara kasar Sin sun kwatanta jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da bishiyar kuka, suna cewa, “Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tamkar bishiyar kuka ce, wadda ke da ingantattun saiwoyi da ma babban karfi na warkar da kanta, tana ta fid da furanni da ‘ya’ya ba tare da tsayawa ba” “bishiyoyin kuka suna da tsawon rai na sama da shekaru dubu”. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana cikin karfinta, kuma za ta ci gaba da kokartawa domin bauta wa jama’a, tare da dogara da jama’a don cimma karin nasarori.

 

Jks
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Jks
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.