• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

In Gwamnati Ta Yi Mana Dam A Hunkuyi  Za Mu Wadata Nijeriya Da Dankalin Turawa -Umaru Dikko

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
In Gwamnati Ta Yi Mana Dam A Hunkuyi  Za Mu Wadata Nijeriya Da Dankalin Turawa -Umaru Dikko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu karatunmu a wannan shafi na noma wanda masu iya magana kan ce, tushen arziki, makon, Wakilinmu Sabo Ahmad Kafin-Maiyaki ya yi tattaki, zuwa wata gona da ke garin Hunkuyi, karamar hukumar Kudan jihar Kaduna, inda ya tattauna da wani shaharren manomin rani, mai suna Alhaji Umaru Dikko wanda a tattaunawar ta su, ya bayyana, bukatar da masu noman rani a wannan yanki ke da ita, wadda za ta taimake su wajen bunkasa noman nasu domin wadata kasa da abinci da samar da aikin yi ga dimbin matasa.

Ga dai yadda tattaunawar ta mu ta gudana, a gonar ta sa da ke garin Hunkuyi, ranar Lahadin da ta gabata.

  • Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati
  • Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

Masu Karatunmu Za Su So Ka Gabatar Da Kanka.

Sunanan Alhaji Umaru Dikkon, ina zaune a cikin garin Hunkuyi, ni manomi ne, musamman na fi bayar da karfi a noman rani, wanda kamar yadda kake gani a halin yanzu a wannan gona tawa, wadda take a nan garib Hunkuyi.

Me Da Me Kake Noma wa A Wannan Gona Taka?

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Ina noma kabeji, amma, babban abin da na fi noma was hi ne, dankalin Turawa.

Daga Ina Kuke Samun Wannan Irin?

Muna samun wannan irin ne daga Jos, amma saboda yanayin kyan kasarmu, har na mu a wasu lokutan yakan fi na Jos din kyau.

Iri Nawa Ne Nau’ukan Dankalin Da Kuke Dasa Wa?

A kalla muna noma dankali nau’in kola da daimon, wadanda dukkan wadannan nau’in dankalin suna yin girma a wannan kasa ta mu, har ma wasu wadanda ban ambata ba.

Shin Wai Shi Dankali Ya Ake Shuka Shi Ne?

Ita kwayar dankalin ake yanka wa sai a dasa a kasa daga nan zai kama sai ya ci gaba da rayuwa, sannan sai a yimasa noma daga nan sai in ya yi a hake shi.

Wane Lokaci Ne Ake Fara Dasa Shi?

Da zara ruwan sama ya dauke ne ake fara dasa shi, a cikin shekara daya mukan dasa shi sau biyu, yanzu haka ma bayan na ranin har zan damina muna yi, muna amfani da takin zamani na NPK 15-15-15 da kuma Uriya, amma kuma wanda ya yi amfani da takin gida sai ya fi samun amfani mai yawa.

Yaya Batun Kasuwar Dankalin?

Babbar matsalar da muke fama da ita, ita ce, yadda za nu adana shi, saboda haka da zarar ya zo dole, mu dayar da shi, duk yadda ta kama.

Wane Kira Kake Da shi Ga Gwamnati?

Kirana na farko shi ne, ta samar mana da kasuwa sai abu na biyu gwamnati ta samar mana da takin zamani abu na uku kuma shi ne gwamnati ta samar mana da dam, wanda za mu yi amfani da shi domin yin ban-ruwa sannan kuma karshe, idan muka samu wannan, noman dankalin Turawa da ma sauran nau’ukan amfani zai habaka a wannanan yanki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DamDankalin TurawaHunkuyiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

Next Post

Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

2 days ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.