• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

In Gwamnati Ta Yi Mana Dam A Hunkuyi  Za Mu Wadata Nijeriya Da Dankalin Turawa -Umaru Dikko

by Abubakar Abba
3 years ago
Dam

Masu karatunmu a wannan shafi na noma wanda masu iya magana kan ce, tushen arziki, makon, Wakilinmu Sabo Ahmad Kafin-Maiyaki ya yi tattaki, zuwa wata gona da ke garin Hunkuyi, karamar hukumar Kudan jihar Kaduna, inda ya tattauna da wani shaharren manomin rani, mai suna Alhaji Umaru Dikko wanda a tattaunawar ta su, ya bayyana, bukatar da masu noman rani a wannan yanki ke da ita, wadda za ta taimake su wajen bunkasa noman nasu domin wadata kasa da abinci da samar da aikin yi ga dimbin matasa.

Ga dai yadda tattaunawar ta mu ta gudana, a gonar ta sa da ke garin Hunkuyi, ranar Lahadin da ta gabata.

  • Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati
  • Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

Masu Karatunmu Za Su So Ka Gabatar Da Kanka.

Sunanan Alhaji Umaru Dikkon, ina zaune a cikin garin Hunkuyi, ni manomi ne, musamman na fi bayar da karfi a noman rani, wanda kamar yadda kake gani a halin yanzu a wannan gona tawa, wadda take a nan garib Hunkuyi.

Me Da Me Kake Noma wa A Wannan Gona Taka?

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Ina noma kabeji, amma, babban abin da na fi noma was hi ne, dankalin Turawa.

Daga Ina Kuke Samun Wannan Irin?

Muna samun wannan irin ne daga Jos, amma saboda yanayin kyan kasarmu, har na mu a wasu lokutan yakan fi na Jos din kyau.

Iri Nawa Ne Nau’ukan Dankalin Da Kuke Dasa Wa?

A kalla muna noma dankali nau’in kola da daimon, wadanda dukkan wadannan nau’in dankalin suna yin girma a wannan kasa ta mu, har ma wasu wadanda ban ambata ba.

Shin Wai Shi Dankali Ya Ake Shuka Shi Ne?

Ita kwayar dankalin ake yanka wa sai a dasa a kasa daga nan zai kama sai ya ci gaba da rayuwa, sannan sai a yimasa noma daga nan sai in ya yi a hake shi.

Wane Lokaci Ne Ake Fara Dasa Shi?

Da zara ruwan sama ya dauke ne ake fara dasa shi, a cikin shekara daya mukan dasa shi sau biyu, yanzu haka ma bayan na ranin har zan damina muna yi, muna amfani da takin zamani na NPK 15-15-15 da kuma Uriya, amma kuma wanda ya yi amfani da takin gida sai ya fi samun amfani mai yawa.

Yaya Batun Kasuwar Dankalin?

Babbar matsalar da muke fama da ita, ita ce, yadda za nu adana shi, saboda haka da zarar ya zo dole, mu dayar da shi, duk yadda ta kama.

Wane Kira Kake Da shi Ga Gwamnati?

Kirana na farko shi ne, ta samar mana da kasuwa sai abu na biyu gwamnati ta samar mana da takin zamani abu na uku kuma shi ne gwamnati ta samar mana da dam, wanda za mu yi amfani da shi domin yin ban-ruwa sannan kuma karshe, idan muka samu wannan, noman dankalin Turawa da ma sauran nau’ukan amfani zai habaka a wannanan yanki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.