ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

In Gwamnati Ta Yi Mana Dam A Hunkuyi  Za Mu Wadata Nijeriya Da Dankalin Turawa -Umaru Dikko

by Abubakar Abba
4 years ago
Dam

Masu karatunmu a wannan shafi na noma wanda masu iya magana kan ce, tushen arziki, makon, Wakilinmu Sabo Ahmad Kafin-Maiyaki ya yi tattaki, zuwa wata gona da ke garin Hunkuyi, karamar hukumar Kudan jihar Kaduna, inda ya tattauna da wani shaharren manomin rani, mai suna Alhaji Umaru Dikko wanda a tattaunawar ta su, ya bayyana, bukatar da masu noman rani a wannan yanki ke da ita, wadda za ta taimake su wajen bunkasa noman nasu domin wadata kasa da abinci da samar da aikin yi ga dimbin matasa.

Ga dai yadda tattaunawar ta mu ta gudana, a gonar ta sa da ke garin Hunkuyi, ranar Lahadin da ta gabata.

  • Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati
  • Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

Masu Karatunmu Za Su So Ka Gabatar Da Kanka.

ADVERTISEMENT

Sunanan Alhaji Umaru Dikkon, ina zaune a cikin garin Hunkuyi, ni manomi ne, musamman na fi bayar da karfi a noman rani, wanda kamar yadda kake gani a halin yanzu a wannan gona tawa, wadda take a nan garib Hunkuyi.

Me Da Me Kake Noma wa A Wannan Gona Taka?

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ina noma kabeji, amma, babban abin da na fi noma was hi ne, dankalin Turawa.

Daga Ina Kuke Samun Wannan Irin?

Muna samun wannan irin ne daga Jos, amma saboda yanayin kyan kasarmu, har na mu a wasu lokutan yakan fi na Jos din kyau.

Iri Nawa Ne Nau’ukan Dankalin Da Kuke Dasa Wa?

A kalla muna noma dankali nau’in kola da daimon, wadanda dukkan wadannan nau’in dankalin suna yin girma a wannan kasa ta mu, har ma wasu wadanda ban ambata ba.

Shin Wai Shi Dankali Ya Ake Shuka Shi Ne?

Ita kwayar dankalin ake yanka wa sai a dasa a kasa daga nan zai kama sai ya ci gaba da rayuwa, sannan sai a yimasa noma daga nan sai in ya yi a hake shi.

Wane Lokaci Ne Ake Fara Dasa Shi?

Da zara ruwan sama ya dauke ne ake fara dasa shi, a cikin shekara daya mukan dasa shi sau biyu, yanzu haka ma bayan na ranin har zan damina muna yi, muna amfani da takin zamani na NPK 15-15-15 da kuma Uriya, amma kuma wanda ya yi amfani da takin gida sai ya fi samun amfani mai yawa.

Yaya Batun Kasuwar Dankalin?

Babbar matsalar da muke fama da ita, ita ce, yadda za nu adana shi, saboda haka da zarar ya zo dole, mu dayar da shi, duk yadda ta kama.

Wane Kira Kake Da shi Ga Gwamnati?

Kirana na farko shi ne, ta samar mana da kasuwa sai abu na biyu gwamnati ta samar mana da takin zamani abu na uku kuma shi ne gwamnati ta samar mana da dam, wanda za mu yi amfani da shi domin yin ban-ruwa sannan kuma karshe, idan muka samu wannan, noman dankalin Turawa da ma sauran nau’ukan amfani zai habaka a wannanan yanki.

Dam
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.