• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Kiran Binani Da APC Su Mara Wa Fintiri Baya – Farauta

by Sadiq
2 years ago
Binani

Biyo bayan hukuncin kotun kolin Nijeriya kan karar da ‘yar takarar gwamnan jam’iyyar APC, Aishatu Dahiru Binani ta daukaka, mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa Kaletapwa G. Farauta, ta bukaci Binani da ta goyi bayan gwamna Ahmadu Umaru Finitri.

Farauta, ta kuma gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’in samun nasarar da suka rika yi wa gwamnatin bisa imanin da karfin gwiwar da suke dashi a kanta.

  • Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS
  • Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Ahmadu Fintiri

Ta ce “Yanzu duk shari’a ta kare, za a kara ganin yadda ake gudanar da mulki, za a mayar da hankali ga samar da ingantacciyar gwamnati a Adamawa” in ji Farauta.

Mataimakiyar gwamnan, wacce ke magana a gidan gwamnatin jihar tare da kakakin majalisar dokokin jihar, da sauran mukaraban gwamnati, ta gode wa bangaren shari’a, ta kuma jaddada bukatar samun hadin kai da goyon bayan jama’ar jihar domin ciyar da jihar gaba.

“Ina kira ga al’ummar Adamawa da su hada kai da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa kudurinsa na ganin jihar ta samu zaman lafiya da ci gaba ta hanyar tsarin gwamnati na jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

“Jama’ar Adamawa iyali guda ne, jiharmu ce baki daya, mu kyale batun jam’iyyarmu, Addini da bambancin kabilanci domin samun ci gaban jiharmu.”

Da ta ke magana kan zaman kotun na ranar Laraba, ta ce “Dama Aishatu Binani ta jam’iyyar APC, ta garzaya kotun kan zaben gwamnan 2023, ta bukaci kotu ta tabbatar da hukuncin da dakataccen kwamishinan zaben hukumar zaben jihar Hudu Yunusa Ari, ya bayyana ta a matsayin wacce ta lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

“Kotun Koli mai mutum biyar karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro, ta amince da hukuncin da kananan kotunan baya suka yanke, inda suka bayyana abin da kwamishinan zabe Hudu Ari ya yi a matsayin mummunan aiki.

“Kotun kolin ta lura da cewa batun shi ne, na wanda ya lashe zabe da mafi yawan kuri’u, na gaskiya, kuma babu wani abu a gaban kotun daukaka kara da ke nuna cewa wanda ake kara na biyu (gwamna Fintiri), bai samu kuri’u mafi rinjaye na gaskiya ba.

“Don haka ta amince da hukuncin kotun daukaka kara, saboda haka ta yi watsi da karar” in ji Farauta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 
Manyan Labarai

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da ‘Askarawan’ Zamfara

Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da 'Askarawan' Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.