• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Kiran Binani Da APC Su Mara Wa Fintiri Baya – Farauta

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Ina Kiran Binani Da APC Su Mara Wa Fintiri Baya – Farauta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan hukuncin kotun kolin Nijeriya kan karar da ‘yar takarar gwamnan jam’iyyar APC, Aishatu Dahiru Binani ta daukaka, mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa Kaletapwa G. Farauta, ta bukaci Binani da ta goyi bayan gwamna Ahmadu Umaru Finitri.

Farauta, ta kuma gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’in samun nasarar da suka rika yi wa gwamnatin bisa imanin da karfin gwiwar da suke dashi a kanta.

  • Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS
  • Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Ahmadu Fintiri

Ta ce “Yanzu duk shari’a ta kare, za a kara ganin yadda ake gudanar da mulki, za a mayar da hankali ga samar da ingantacciyar gwamnati a Adamawa” in ji Farauta.

Mataimakiyar gwamnan, wacce ke magana a gidan gwamnatin jihar tare da kakakin majalisar dokokin jihar, da sauran mukaraban gwamnati, ta gode wa bangaren shari’a, ta kuma jaddada bukatar samun hadin kai da goyon bayan jama’ar jihar domin ciyar da jihar gaba.

“Ina kira ga al’ummar Adamawa da su hada kai da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa kudurinsa na ganin jihar ta samu zaman lafiya da ci gaba ta hanyar tsarin gwamnati na jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

“Jama’ar Adamawa iyali guda ne, jiharmu ce baki daya, mu kyale batun jam’iyyarmu, Addini da bambancin kabilanci domin samun ci gaban jiharmu.”

Da ta ke magana kan zaman kotun na ranar Laraba, ta ce “Dama Aishatu Binani ta jam’iyyar APC, ta garzaya kotun kan zaben gwamnan 2023, ta bukaci kotu ta tabbatar da hukuncin da dakataccen kwamishinan zaben hukumar zaben jihar Hudu Yunusa Ari, ya bayyana ta a matsayin wacce ta lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

“Kotun Koli mai mutum biyar karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro, ta amince da hukuncin da kananan kotunan baya suka yanke, inda suka bayyana abin da kwamishinan zabe Hudu Ari ya yi a matsayin mummunan aiki.

“Kotun kolin ta lura da cewa batun shi ne, na wanda ya lashe zabe da mafi yawan kuri’u, na gaskiya, kuma babu wani abu a gaban kotun daukaka kara da ke nuna cewa wanda ake kara na biyu (gwamna Fintiri), bai samu kuri’u mafi rinjaye na gaskiya ba.

“Don haka ta amince da hukuncin kotun daukaka kara, saboda haka ta yi watsi da karar” in ji Farauta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaBinaniFintiriKotun KoliZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS

Next Post

Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da ‘Askarawan’ Zamfara

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

8 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

10 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

12 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

15 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

17 hours ago
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da ‘Askarawan’ Zamfara

Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da 'Askarawan' Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.