ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Kiran Binani Da APC Su Mara Wa Fintiri Baya – Farauta

by Sadiq
2 years ago
Binani

Biyo bayan hukuncin kotun kolin Nijeriya kan karar da ‘yar takarar gwamnan jam’iyyar APC, Aishatu Dahiru Binani ta daukaka, mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa Kaletapwa G. Farauta, ta bukaci Binani da ta goyi bayan gwamna Ahmadu Umaru Finitri.

Farauta, ta kuma gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’in samun nasarar da suka rika yi wa gwamnatin bisa imanin da karfin gwiwar da suke dashi a kanta.

  • Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS
  • Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Ahmadu Fintiri

Ta ce “Yanzu duk shari’a ta kare, za a kara ganin yadda ake gudanar da mulki, za a mayar da hankali ga samar da ingantacciyar gwamnati a Adamawa” in ji Farauta.

ADVERTISEMENT

Mataimakiyar gwamnan, wacce ke magana a gidan gwamnatin jihar tare da kakakin majalisar dokokin jihar, da sauran mukaraban gwamnati, ta gode wa bangaren shari’a, ta kuma jaddada bukatar samun hadin kai da goyon bayan jama’ar jihar domin ciyar da jihar gaba.

“Ina kira ga al’ummar Adamawa da su hada kai da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa kudurinsa na ganin jihar ta samu zaman lafiya da ci gaba ta hanyar tsarin gwamnati na jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

“Jama’ar Adamawa iyali guda ne, jiharmu ce baki daya, mu kyale batun jam’iyyarmu, Addini da bambancin kabilanci domin samun ci gaban jiharmu.”

Da ta ke magana kan zaman kotun na ranar Laraba, ta ce “Dama Aishatu Binani ta jam’iyyar APC, ta garzaya kotun kan zaben gwamnan 2023, ta bukaci kotu ta tabbatar da hukuncin da dakataccen kwamishinan zaben hukumar zaben jihar Hudu Yunusa Ari, ya bayyana ta a matsayin wacce ta lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

“Kotun Koli mai mutum biyar karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro, ta amince da hukuncin da kananan kotunan baya suka yanke, inda suka bayyana abin da kwamishinan zabe Hudu Ari ya yi a matsayin mummunan aiki.

“Kotun kolin ta lura da cewa batun shi ne, na wanda ya lashe zabe da mafi yawan kuri’u, na gaskiya, kuma babu wani abu a gaban kotun daukaka kara da ke nuna cewa wanda ake kara na biyu (gwamna Fintiri), bai samu kuri’u mafi rinjaye na gaskiya ba.

“Don haka ta amince da hukuncin kotun daukaka kara, saboda haka ta yi watsi da karar” in ji Farauta.

MASU ALAKA

kebbi
Labarai

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da ‘Askarawan’ Zamfara

Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da 'Askarawan' Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

July 9, 2026
Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

July 9, 2026
Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.