ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Kiran Binani Da APC Su Mara Wa Fintiri Baya – Farauta

by Sadiq
2 years ago
Binani

Biyo bayan hukuncin kotun kolin Nijeriya kan karar da ‘yar takarar gwamnan jam’iyyar APC, Aishatu Dahiru Binani ta daukaka, mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa Kaletapwa G. Farauta, ta bukaci Binani da ta goyi bayan gwamna Ahmadu Umaru Finitri.

Farauta, ta kuma gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’in samun nasarar da suka rika yi wa gwamnatin bisa imanin da karfin gwiwar da suke dashi a kanta.

  • Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Ficewar Nijar, Mali Da Burkina Faso Daga ECOWAS
  • Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Nasarar Gwamna Ahmadu Fintiri

Ta ce “Yanzu duk shari’a ta kare, za a kara ganin yadda ake gudanar da mulki, za a mayar da hankali ga samar da ingantacciyar gwamnati a Adamawa” in ji Farauta.

ADVERTISEMENT

Mataimakiyar gwamnan, wacce ke magana a gidan gwamnatin jihar tare da kakakin majalisar dokokin jihar, da sauran mukaraban gwamnati, ta gode wa bangaren shari’a, ta kuma jaddada bukatar samun hadin kai da goyon bayan jama’ar jihar domin ciyar da jihar gaba.

“Ina kira ga al’ummar Adamawa da su hada kai da gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, bisa kudurinsa na ganin jihar ta samu zaman lafiya da ci gaba ta hanyar tsarin gwamnati na jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Jama’ar Adamawa iyali guda ne, jiharmu ce baki daya, mu kyale batun jam’iyyarmu, Addini da bambancin kabilanci domin samun ci gaban jiharmu.”

Da ta ke magana kan zaman kotun na ranar Laraba, ta ce “Dama Aishatu Binani ta jam’iyyar APC, ta garzaya kotun kan zaben gwamnan 2023, ta bukaci kotu ta tabbatar da hukuncin da dakataccen kwamishinan zaben hukumar zaben jihar Hudu Yunusa Ari, ya bayyana ta a matsayin wacce ta lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

“Kotun Koli mai mutum biyar karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro, ta amince da hukuncin da kananan kotunan baya suka yanke, inda suka bayyana abin da kwamishinan zabe Hudu Ari ya yi a matsayin mummunan aiki.

“Kotun kolin ta lura da cewa batun shi ne, na wanda ya lashe zabe da mafi yawan kuri’u, na gaskiya, kuma babu wani abu a gaban kotun daukaka kara da ke nuna cewa wanda ake kara na biyu (gwamna Fintiri), bai samu kuri’u mafi rinjaye na gaskiya ba.

“Don haka ta amince da hukuncin kotun daukaka kara, saboda haka ta yi watsi da karar” in ji Farauta.

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da ‘Askarawan’ Zamfara

Matsalar Tsaro: Gwamna Dauda Ya Kaddamar Da 'Askarawan' Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.