• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban limamin masallacin Abuja, Farfesa Ibrahim Ahmad Makari ya bayyana cewa yana nan kan ra’ayinsa bai yarda malami ya shiga siyasa ba, amma yana so a bambanta abubuwa guda biyu.

“Bana sha’awar malami ya shiga siyasa daban, amma idan ya kasance wannan malamin yana da wasu ilimi na rayuwa wanda ya shahara a kai, idan har ya shiga siyasa to ko ya yi kuskure ba za a danganta wannan kuskuren da addini ba. Abin da ake nufi dai ilimi ne kadai abin da ake bukata.”

  • Zan Bayyana Dan Takarar Da Zan Mara Wa Baya A Janairu – Wike
  • An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Farfesa Makari ya kara da cewa akwai hakkin shugaba a kan talakawa, haka kuma akwai hakkin talakawa a kan shugaba wanda suka hada da biyyaya da kuma adalci.

Ya ce wannan zabe da za a gudanar shaida ce da Allah zai taimaya a kai ranar Lahira. Ya ce duk wanda ka zaba kar ka dauka abin wasa, kamar yadda ake raba wa mutane kudi ko omo domin su zabi mutum. A cewarsa, wannan kudi ko omo da aka ba ka domin yin zabe, ka tabbatar da cewa shaida ce wanda Allah zai tambaye ka a ranar tashin kiya.

Farfasa Makari ya shawarci mutane su duba wadanda suka fi yi musu zaton alkairi kamar yin adalci, tausaya wa al’umma, to ka gina zabenka a kan wannan turbali na zaben shugaba. Ya ce lallai mutane su duba wanda zai fi yi wa al’umma abubuwan da suka kamata a zaben shugaba domin su, sai ka yi kokarin gina zabenka a kan wannan ma’auni, amma duk lokacin da al’umma suka makantar da idanuwansu da hankulansu suka gina zabensu kan yadda mutane ke dibar miliyoyin kudade suna wazawa domin a zabesu har su hau wasu mukamai a kan su magance matsaloli, to lallai ba a shirya ganin lokacin magance matsalilin ba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya ce ba zai taba iya fahimtar kishin kasa da za ta sa mutum ya dunga kwaso kudi yana kokarin sayan kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta ba.

“Ni dai a fahimtata na kasa gane wannan kishin kasa wanda mutum zai kwaso kudi yana rabawa domin ya sayi kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta.”

Farfasa Makari ya ce, “Akwai kalubale mai girma a gabanmu, abun da ake fadi na cewa ko ka zaba ko baka zaba ba za a zaben maka, wannan magana ba gaskiya ba ce. Lallai wanda zai shugabanci al’umma, yanke hukunci na karshe yana hannun al’umma ne wanda suka bi layi domin zaban wanda zai shugabance su.

“Kaurace wa zabe, mutum ya ce ba zai yi zabe ba saboda wasu dalilai, to zai iya zama kara taimakon masu barna a kan barnar. Saboda ko ka yi zabe ko ba ka yi ba a ranar da za a rantsar da shugaba dole ne a rantsar da shi. Domin rashin zaben ka ba zai sa a kasa rantar da wanda za a rantsar ba.

“Saboda haka, ‘yan’uwa mu yi kokari mu zabi cancanta. Ka da mu mayar da kanmu koma-bayan da wani ya ce mana ku zabi wane, domin muna da hankular kanmu. Sannan kar mu gina zabenmu a kan jam’iyya, dama a farkon maganana na fadi cewa damokuradiyyar nan iya kokarinta take yi ta yi abin da yake daidai, amma karka dauka komi nata daidai ne.

“Idan mutum ya ce maka jam’iyya kaza za ka zaba daga sama har kasa domin ra’ayinsa wanda ba ita ce daidai ba, kai kuma ka duba cancata. Ya kamata mu gane babu wata jam’iyya a yanzu, domin ‘yan takara nawa ne suka sauya sheka wanda har wurin kamfen suna kuskuran iya fadin jam’iyyarsu, saboda sabawa wanda ya kasance jiya suke can, yanzu kuma suna nan, wanda hakan ne ya sa suke kuskuren fadin sunan jam’iyyunsu.

“Bai kamata ana ci gaba da yawo da hankalinmu ba, ya kamata mu yi kokarin gina zabenmu a kan wadanda suka cancanta,” in ji Farfasa Makari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Farfesa MakariMalamiSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutun Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Next Post

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Malami
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana'a Ba A Bauchi" —Sadique

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.