• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban limamin masallacin Abuja, Farfesa Ibrahim Ahmad Makari ya bayyana cewa yana nan kan ra’ayinsa bai yarda malami ya shiga siyasa ba, amma yana so a bambanta abubuwa guda biyu.

“Bana sha’awar malami ya shiga siyasa daban, amma idan ya kasance wannan malamin yana da wasu ilimi na rayuwa wanda ya shahara a kai, idan har ya shiga siyasa to ko ya yi kuskure ba za a danganta wannan kuskuren da addini ba. Abin da ake nufi dai ilimi ne kadai abin da ake bukata.”

  • Zan Bayyana Dan Takarar Da Zan Mara Wa Baya A Janairu – Wike
  • An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Farfesa Makari ya kara da cewa akwai hakkin shugaba a kan talakawa, haka kuma akwai hakkin talakawa a kan shugaba wanda suka hada da biyyaya da kuma adalci.

Ya ce wannan zabe da za a gudanar shaida ce da Allah zai taimaya a kai ranar Lahira. Ya ce duk wanda ka zaba kar ka dauka abin wasa, kamar yadda ake raba wa mutane kudi ko omo domin su zabi mutum. A cewarsa, wannan kudi ko omo da aka ba ka domin yin zabe, ka tabbatar da cewa shaida ce wanda Allah zai tambaye ka a ranar tashin kiya.

Farfasa Makari ya shawarci mutane su duba wadanda suka fi yi musu zaton alkairi kamar yin adalci, tausaya wa al’umma, to ka gina zabenka a kan wannan turbali na zaben shugaba. Ya ce lallai mutane su duba wanda zai fi yi wa al’umma abubuwan da suka kamata a zaben shugaba domin su, sai ka yi kokarin gina zabenka a kan wannan ma’auni, amma duk lokacin da al’umma suka makantar da idanuwansu da hankulansu suka gina zabensu kan yadda mutane ke dibar miliyoyin kudade suna wazawa domin a zabesu har su hau wasu mukamai a kan su magance matsaloli, to lallai ba a shirya ganin lokacin magance matsalilin ba.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Ya ce ba zai taba iya fahimtar kishin kasa da za ta sa mutum ya dunga kwaso kudi yana kokarin sayan kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta ba.

“Ni dai a fahimtata na kasa gane wannan kishin kasa wanda mutum zai kwaso kudi yana rabawa domin ya sayi kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta.”

Farfasa Makari ya ce, “Akwai kalubale mai girma a gabanmu, abun da ake fadi na cewa ko ka zaba ko baka zaba ba za a zaben maka, wannan magana ba gaskiya ba ce. Lallai wanda zai shugabanci al’umma, yanke hukunci na karshe yana hannun al’umma ne wanda suka bi layi domin zaban wanda zai shugabance su.

“Kaurace wa zabe, mutum ya ce ba zai yi zabe ba saboda wasu dalilai, to zai iya zama kara taimakon masu barna a kan barnar. Saboda ko ka yi zabe ko ba ka yi ba a ranar da za a rantsar da shugaba dole ne a rantsar da shi. Domin rashin zaben ka ba zai sa a kasa rantar da wanda za a rantsar ba.

“Saboda haka, ‘yan’uwa mu yi kokari mu zabi cancanta. Ka da mu mayar da kanmu koma-bayan da wani ya ce mana ku zabi wane, domin muna da hankular kanmu. Sannan kar mu gina zabenmu a kan jam’iyya, dama a farkon maganana na fadi cewa damokuradiyyar nan iya kokarinta take yi ta yi abin da yake daidai, amma karka dauka komi nata daidai ne.

“Idan mutum ya ce maka jam’iyya kaza za ka zaba daga sama har kasa domin ra’ayinsa wanda ba ita ce daidai ba, kai kuma ka duba cancata. Ya kamata mu gane babu wata jam’iyya a yanzu, domin ‘yan takara nawa ne suka sauya sheka wanda har wurin kamfen suna kuskuran iya fadin jam’iyyarsu, saboda sabawa wanda ya kasance jiya suke can, yanzu kuma suna nan, wanda hakan ne ya sa suke kuskuren fadin sunan jam’iyyunsu.

“Bai kamata ana ci gaba da yawo da hankalinmu ba, ya kamata mu yi kokarin gina zabenmu a kan wadanda suka cancanta,” in ji Farfasa Makari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Farfesa MakariMalamiSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutun Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Next Post

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

2 days ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

2 days ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana'a Ba A Bauchi" —Sadique

LABARAI MASU NASABA

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.