ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

by Leadership Hausa
7 months ago
INEC

Mai Magana da yawun TNN, Dakta Mohammed Adah Shaibu, ya bayyana cewa ana kara yi wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) matsin lamba daga manyan bangarori daban-daban don ka da a yi wa TNN rajista a matsayin jam’iyyar siyasa a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da aka gabatar wa manema labarai da mai magana da yawun TNN ya rattaba hannu a Kaduna, ya bayyana cewa kungiyar ta nemi yin rajista na zamowa jam’iyyar siyasa tun a shekarar 2024.

  • ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo
  • Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi

A cewar sanarwar, an gabatar da bukatar yin rajista ga INEC kuma an amince da ita tun ranar 27 ga Mayun 2024.

ADVERTISEMENT

Ya nuna takaicinsa cewa, “Tun lokacin da aka gabatar da bukatar yin rajista, INEC kawai ta rubuta wasikar amincewa tana alkawarin sanar da su lokacin da za a bude yi rajista don gabatar da takardu, kuma duk kokarin da aka yi don tunatar da Shugaban INEC, Farfesa Yakubu Mahmoud game da kundin tsarin mulki da dokar zabe suka tabbatar ya yi watsi da shi, duk da cewa an wuce wa’adin kwanaki 90, lokacin da aka tilsata wa hukumar mayar da sakon kan wasikar da aka shigar mata.

“Har yaushe za mu jira kafin mu yi rajista? Kasancewar mu a duk fadin kasar nan kuma muna da karancin lokaci don isar da manufofinmu na siysa ga masu jefa kuri’a.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

“Babu shakka cewa INEC na fuskantar matsin lamba mai tsanani, daga mambobin APC da sauran abokan huldarsu wadanda ke tsoron TNN, domin sun shirya yin magudi a zaben 2027 wajen samun nasararsu.

“Amma muna kira ga INEC da ka da ta bayar da kai bori ya hau a matsayinta na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa tare da kare mutuncnta ta hanyar kin yin abin da ya saba wa doka. 

“Muna tunatar da hukumar INEC cewa ‘yan Nijeriya suna sa ido sosai kan yadda za ta magance wannan batun na TNN, kuma duk abin da za ta yi zai tantance ko ‘yan Nijeriya za su iya dogaro da ita don shirya sahihin zabbe mai cike da adalci a 2027,” in ji sanarwar.

Ya kuma ce, “Idan aka yi la’akari da siyasar da ta riga ta wuce gona da iri gabanin zaben 2027, mun yi imanin INEC ba za ta yi wani abu da zai kara ta’azzara lamarin ba”.

Ya bukaci INEC da ta bi ka’idojinta da kuma kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, wanda hakan zai ba da damar kungiyarsa ta yi rajista a matsayin jam’iyyar siyasa daidai da dokokin kasar da kuma yin takara a dukkan matakai daga kananan hukumomi a babban zabe mai zuwa.

A halin da ake ciki, TNN ta yi kira ga dukkan magoya bayanta su kwantar da hankulansu kan batun yin rajista.

“Mun san cewa da yawa daga cikin magoya bayanmu masu yawa sun fusata da rahoton matsin lambar da ake yi wa INEC kan wannan batun. Amma dole ne su ci gaba da bin doka da oda yayin da muke jiran hukuncin INEC.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.