ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bai Wa Zababben Gwamnan Kebbi Takardar Shaidar Lashe Zabe

by Sadiq
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), a Jihar Kebbi, ta bayar da takardar shaidar lashe zabe ga zababben gwamnan jihar, Nasir Idris da mataimakinsa Umar Abubakar da ‘yan majalisar dokokin jihar 10.

Farfesa Muhammad Sani Kalla, Kwamishinan INEC na kasa mai kula da jihohin Sokoto, Kebbi da Zamfara, ya kuma bayar da takardar shaidar cin zabe ga wasu zababbun ‘yan majalisar dokokin jihar a zaben da aka kammala.

  • An Kwaso ‘Yan Nijeriya 107 Da Suka Makale A Libya
  • Buhari Ya Yi Wa Shugaban NIS Jere Ritaya

Jihar na da mazabu 24 na jihar sannan kuma INEC a ranar 30 ga watan Maris ta gabatar da takardar shaidar cin zabe ga mutane 14 da suka yi nasara a zaben majalisar dokokin jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

ADVERTISEMENT

Dokta Nasir Idris jim kadan bayan karbar satifiket dinsa, ya yabawa hukumar, da hukumomin tsaro bisa yadda jama’a suka gudanar da zabe ba tare da wata matsala ba a cikin fadin jihar baki daya.

Ya kuma mika godiyarsa ga wadanda suka zabe su bisa yadda suka tabbatar da an gudanar da aikin cikin nasara tare da wata matsala ba, ya roki Allah da ya ba su ikon yiwa al’amuransu adalci a yayin tafiyar da mulki a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Haka Kuma ya ce ” jihar Kebbi tana da albarkatun kasa, kuma za mu yi duk abin da ya kamata na dan Adam wajen amfani da wadannan albarkatun domin ci gaban al’ummar jihar.

“Za mu ci gaba da gudanar da ayyukan da gwamnati mai ci ke gudanarwa kafin mu tsunduma cikin sababbi. Za mu samar da guraben ayyukan yi da yawa ga jama’a, musamman a fannin noma.

“ A bangaren tsaro za mu yi duk mai yiwuwa wajen maido da tsaro a yankunan da rikicin ya shafa a Kudancin jihar, domin al’ummar yankin su je gonakinsu daban-daban da kuma samar da abinci mai yawa da kuma bunkasa samar da abinci a jihar da kasa baki daya.

“Za mu cika dukkan alkawuran da muka yi wa jama’a a lokacin yakin neman zabe a jihar idan Allah ya kaimu.

Daga karshe ya bukace su da su yi addu’ar samun nasarar ga gwamnatin sa.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Next Post
INEC Za Ta Bai Wa Fintiri Shaidar Lashe Zabe Yau

INEC Za Ta Bai Wa Fintiri Shaidar Lashe Zabe Yau

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.