ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

by Leadership Hausa
1 year ago
Aiki

Tsarin Nijeriya ya nuna cewa, kasa ce, mai ala’adu iri da ban da ban wadda kuma take dauke da wasu jama’a da ke aikata, manyan laifuka.

A bisa irin wannan yanayin ne, akawai bukatar a hada kai tare a yi aiki tare da hukumomin tsaro na kasar.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

Duba da cewa, hukumomin tsaro a kasar na ci gaba da rike ayyukansu na sirrin tsaro, musamman saboda gasar da suke yi da sauran hukumomin tsaro na kasar domin kar su shiga bansu, wajen gudanr da ayyukansu, na samar da tsaro.

ADVERTISEMENT

Sai dai, ya zama wajbi, a kawo karshen irin wannan gasar da ke a tsakanin hukumomin tsaron, matukar dai, ana bukatar a kawo karshen kalubalen rashin tsaro da ke ci gaba da addamar Nijeriya.

Bisa dokar Nijeriya Cap 278 ta shekarar 1986, kasar ta kasance ta na da hukumomin tsaro na sirri guda uku ne, bayan rusa rundunar hukumar tsaro ta kasa wato NSO.

LABARAI MASU NASABA

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

Hukumomin tsaron uku su ne, na DIA, DSS da kuma NIA, inda kuma dokar, ta bayar da damar kafa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro wato ONSA, wadda a baya, ake kiran ofishin da Babban Jami’in Tsaro na Kasa wato CONS.

Wannan Jaridar, na nuna matukar damauwarta kan ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fuskata, musamman na rashin gazawar hukumomin tsaro na sirri saboda gasar da suke nuna wa, a tsakaninsu.

A bisa ra’ayinmu, wannan matsalar, abu ne da ke bukatar a kara mayar da hankali cikin gaggawa domin a magance wannan kalubalen na rashin na rashin tsaron.

Sai dai, muna kuma yabawa kokarin da hukumomin tsaron ke ci gaba da yi, na lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaro.

Amma abin takaici ne, kan yadda gasar a tsakanin hukumomin tsaron kasar, ke kara haifar da kalubalen na rashin tsaro wanda kamata ya yi ace, suna yin aiki tare, domin a samar wa da ‘yan Nijeriya sauki, wajen magance masu kalubalen rashin tsaron, da suke ci gaba da fuskanta.

Hatta shi ma tsohon Babban Hafsan Tasron kasar ya tabbatar da cewa, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su kara zagaewa wajen samar da dabarun kara ciyar da hukumomin na tsaro.

Wasu kwararru na ganin cewa, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin samar da tsaro a kasar.

Gasar da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin hukomomin tsaron su kasance suna samar da bayanan sirri a tsakaninsu, domin a dakile kalubalen rashin tsaro a kasar.

Masu ruwa da tsaki a kasar, ciki har da shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ci gaba da nuna damuwarsu, kan kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da yadda Tinubu, a wani taro na kwanan baya ya sanar da cewa, kalubalen rashin tsaro a karni na 21, abu ne da ake bukatar hada kai, amma ba wai batun nuna yin gasa, a tsakanin hukumomin tsaron kasar ba.

Kalubalen ta’addanci a Arewa Maso Gabas, matsalar ayyukan ‘yan bindiga a Arewa Maso Yamma, fashi a Tekunan ruwa a Tekun Guinea, rikicin manoma da makiyaya a yankin Middle-Belt, batun ‘yan aware a yankin Kudu Maso Gabas, wadannan matsalolin, abu ne, da yafi karfin hukumar tsaro daya, ta kawo karshensu.

Kazalika, hare-haren da suka janoyo kashe wasu kauyawa kimanin su 200 a daren ranar 13 na watan Yunin 2025 yankin Yelwata, na karamar hukumar Guma a jihar Biniwe da kuma sake dawor ayyukan ‘yan ta’addar Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabas, hakan ya nuna a zahiri, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro da kuma kawo karshen sa, musamman duba da cewa, matsalar na kara zama barazana ga tattalin arzikin.

Sai dai, hakan ya nuna cewa, kusan babu wani katabus da hukumomin tsaron ke yi, na magance kalubalen na rashin tsaron.

A ra’ayin wannan Jaridar, akwai matukar bukatar Gwamnati ta dauki kwararan matakai, musamman domin gano ainahin tushen matsalar ta rashin tsaro, da kuma magance ta.

Sai dai, wani kokari daya shi ne, na kara fadada mahukuntan na tsaron sirri wato kafa cibiyar kasa ta dakile yunkurin ayyukan ta’addanci NCTC.

Bukatar hukumomin tsaron na sirri, na yin aiki a tare, abu ne da yake da matukar mahimmanci, musamman domin a magance kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fusanta.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su jingine batun gasa a tsakaninsu, su mayar da hankali, wajen lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaro a kasar.

Kazalika, duba da irin yanayin na barazar rashin tsaron, ya kamata a kara zuba kudade wajen kara darajar kayan kimiyya na aikin tsaro na hukumomin tsaron kasar, wanda hakan zai kara masu kwarin guiwar, kara mayar da hankali a ayyukansu.

Aiki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Aiki

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.