ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

by Leadership Hausa
11 months ago
Aiki

Tsarin Nijeriya ya nuna cewa, kasa ce, mai ala’adu iri da ban da ban wadda kuma take dauke da wasu jama’a da ke aikata, manyan laifuka.

A bisa irin wannan yanayin ne, akawai bukatar a hada kai tare a yi aiki tare da hukumomin tsaro na kasar.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

Duba da cewa, hukumomin tsaro a kasar na ci gaba da rike ayyukansu na sirrin tsaro, musamman saboda gasar da suke yi da sauran hukumomin tsaro na kasar domin kar su shiga bansu, wajen gudanr da ayyukansu, na samar da tsaro.

ADVERTISEMENT

Sai dai, ya zama wajbi, a kawo karshen irin wannan gasar da ke a tsakanin hukumomin tsaron, matukar dai, ana bukatar a kawo karshen kalubalen rashin tsaro da ke ci gaba da addamar Nijeriya.

Bisa dokar Nijeriya Cap 278 ta shekarar 1986, kasar ta kasance ta na da hukumomin tsaro na sirri guda uku ne, bayan rusa rundunar hukumar tsaro ta kasa wato NSO.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Hukumomin tsaron uku su ne, na DIA, DSS da kuma NIA, inda kuma dokar, ta bayar da damar kafa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro wato ONSA, wadda a baya, ake kiran ofishin da Babban Jami’in Tsaro na Kasa wato CONS.

Wannan Jaridar, na nuna matukar damauwarta kan ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fuskata, musamman na rashin gazawar hukumomin tsaro na sirri saboda gasar da suke nuna wa, a tsakaninsu.

A bisa ra’ayinmu, wannan matsalar, abu ne da ke bukatar a kara mayar da hankali cikin gaggawa domin a magance wannan kalubalen na rashin na rashin tsaron.

Sai dai, muna kuma yabawa kokarin da hukumomin tsaron ke ci gaba da yi, na lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaro.

Amma abin takaici ne, kan yadda gasar a tsakanin hukumomin tsaron kasar, ke kara haifar da kalubalen na rashin tsaro wanda kamata ya yi ace, suna yin aiki tare, domin a samar wa da ‘yan Nijeriya sauki, wajen magance masu kalubalen rashin tsaron, da suke ci gaba da fuskanta.

Hatta shi ma tsohon Babban Hafsan Tasron kasar ya tabbatar da cewa, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su kara zagaewa wajen samar da dabarun kara ciyar da hukumomin na tsaro.

Wasu kwararru na ganin cewa, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin samar da tsaro a kasar.

Gasar da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin hukomomin tsaron su kasance suna samar da bayanan sirri a tsakaninsu, domin a dakile kalubalen rashin tsaro a kasar.

Masu ruwa da tsaki a kasar, ciki har da shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ci gaba da nuna damuwarsu, kan kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da yadda Tinubu, a wani taro na kwanan baya ya sanar da cewa, kalubalen rashin tsaro a karni na 21, abu ne da ake bukatar hada kai, amma ba wai batun nuna yin gasa, a tsakanin hukumomin tsaron kasar ba.

Kalubalen ta’addanci a Arewa Maso Gabas, matsalar ayyukan ‘yan bindiga a Arewa Maso Yamma, fashi a Tekunan ruwa a Tekun Guinea, rikicin manoma da makiyaya a yankin Middle-Belt, batun ‘yan aware a yankin Kudu Maso Gabas, wadannan matsalolin, abu ne, da yafi karfin hukumar tsaro daya, ta kawo karshensu.

Kazalika, hare-haren da suka janoyo kashe wasu kauyawa kimanin su 200 a daren ranar 13 na watan Yunin 2025 yankin Yelwata, na karamar hukumar Guma a jihar Biniwe da kuma sake dawor ayyukan ‘yan ta’addar Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabas, hakan ya nuna a zahiri, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro da kuma kawo karshen sa, musamman duba da cewa, matsalar na kara zama barazana ga tattalin arzikin.

Sai dai, hakan ya nuna cewa, kusan babu wani katabus da hukumomin tsaron ke yi, na magance kalubalen na rashin tsaron.

A ra’ayin wannan Jaridar, akwai matukar bukatar Gwamnati ta dauki kwararan matakai, musamman domin gano ainahin tushen matsalar ta rashin tsaro, da kuma magance ta.

Sai dai, wani kokari daya shi ne, na kara fadada mahukuntan na tsaron sirri wato kafa cibiyar kasa ta dakile yunkurin ayyukan ta’addanci NCTC.

Bukatar hukumomin tsaron na sirri, na yin aiki a tare, abu ne da yake da matukar mahimmanci, musamman domin a magance kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fusanta.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su jingine batun gasa a tsakaninsu, su mayar da hankali, wajen lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaro a kasar.

Kazalika, duba da irin yanayin na barazar rashin tsaron, ya kamata a kara zuba kudade wajen kara darajar kayan kimiyya na aikin tsaro na hukumomin tsaron kasar, wanda hakan zai kara masu kwarin guiwar, kara mayar da hankali a ayyukansu.

Aiki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.