• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Siyasa
0
INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta yi kira ga majalisar dokokin ƙasar nan da ta samar da tsauraran dokoki da ke haramta wa ‘yan siyasa zuwa da maƙudan kuɗaɗe a rumfunan zaɓe domin daƙile saye da sayar da ƙuri’u da sauran kura-kurai a lokacin zaɓe.

Wannan kuma na zuwa ne daidai da lokacin da shugaban kwamitin majalisar kan harkokin zabe, Hon. Adebayo Balogun ya sanar da shirin kafa dokar zabe ta 2025 domin maye gurbin na 2022 da ake yi a yanzu, wanda ya ce ya fallasa gibi a zaben 2023.

  • Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027
  • INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe

Da yake jawabi a wajen wani taron tuntuba da jami’an tsaro da kwamitin kwararru kan gyaran dokokin zabe a Abuja ranar Juma’a, Daraktan INEC, Tanimu Muhammed, ya bayyana yadda ake kara nuna damuwa kan sayen kuri’u, wanda ya zama babbar barazana ga tsarin dimokuradiyyar Nijeriya.

Taron wanda kwamitin hadin gwiwa na majalisar dattawa da na wakilai kan harkokin zabe suka shirya tare da hadin gwiwar Cibiyar Bayar da Shawara ta Siyasa (PLAC) da goyon bayan Ofishin Harkokin Wajen Ingila, da kungiyar kasahen rainon Ingila da Ofishin Ci Gaba na Burtaniya (FCDO), ya samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki don tattauna batun tsaro da sauye-sauyen doka.

Wakilin INEC ya lura da cewa ‘yan siyasa kan bayar da hujjar daukar makudan kudade a ranar zabe ta hanyar ba da misali da kudaden da wakilan jam’iyyar ke kashewa da kuma wasu bukatoci. Sai dai kuma ya yi gargadin cewa rashin takaita yawan kudaden da ake zuwa rumfunan zabe da su ya kara rura wutar siyan kuri’u da kuma kawo cikas ga ingancin zabe.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Domin magance wannan kalubale, Muhammed ya ba da shawarar ka da a bar mutane su dauki kudi fiye da naira 50,000 a rumfunan zabe.

“Sayen kuri’u na daya daga cikin manyan barazana ga sahihin zabe a Nijeriya. Muna bukatar dokar da ba wai kawai ta haramta wannan dabi’ar ba har ma da sanya matakan kariya,” in ji Muhammed.

Bayan sayen kuri’u, jami’an INEC sun sake jaddada bukatar da suka dade suna yi na a kafa hukumar da ke yaki da laifukan zabe, suna masu cewa hukumar zabe ba ta da karfin gurfanar da masu laifi a gaban kotu.

A cewar Muhammed, “INEC na iya bakin kokarinta wajen ganin an gurfanar da masu laifukan zabe a gaban kotu, amma muna bukatar wata cibiya mai kwazo da ke da hurumin shari’a da kayan aiki domin gudanar da bincike tare da hukunta masu aikata laifukan zabe. Samar da hukumar zai tabbatar da cewa hukuncin sayen kuri’u, satar kuri’u, da sauran laifuffuka cikin gaggawa”.

Kwamishinan ‘yansanda mai kula da tsare-tsare da tantance harkokin zabe, Abayomi Shogunle, wanda ya wakilci babban sufetan ‘yansanda, ya yi nuni da cewa rashin isassun kayan aiki ya kan kawo cikas ga kokarin tabbatar da doka a lokacin zabe. “Muna fuskantar manyan kalubalen kayan aiki, tun daga tura jami’ai zuwa lunguna da sako da kuma tabbatar da sadarwa a lokacin zabe. Wadannan batutuwa ne da ya kamata a magance su idan ana son a aiwatar da dokokin zabe yadda ya kamata,” in ji Shogunle.

Da yake mayar da martani kan matsalolin da suka taso, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin zabe, Hon. Adebayo Balogun, ya bayar da tabbacin cewa za a magance dukkan batutuwan da aka tattauna tare da sake fasalin zabe a nan gaba.

“Dokar zaben 2022, tana da matukar muhimmin wajen ci gaba, amma aiwatar da ita a babban zaben da ya gabata ya nuna wuraren da ke bukatar gyara. Mun himmatu wajen karfafa dokokin zabenmu don nuna gaskiyar dimokuradiyyarmu,” in ji Balogun.

Ya jaddada cewa, baya ga garambawul na majalisar, akwai bukatar kara wayar da kan jam’iyyun siyasa, jami’an INEC, da kungiyoyin fararen hula kan illolin da ke tattare da sayen kuri’u da sauran kura-kurai a zaɓen ƙasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECZabeZaɓe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministoci Za Su Fara Gabatar Da Rahoton Ayyuka A Taron Manema Labarai  

Next Post

Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

3 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

4 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

5 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi

Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.