• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu ya bukaci a samar da tsaro a dukkanin yankunan da za gudanar da zaben cike gurbi a kasar nan.

Yakubu ya yi wannan kiran ne a lokacin wata ganawa da kwamitin samar da tsaro kan zabe a Abuja.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Ya bayyana cewa akwai zaben da za a yi a watan Fabrairu har kashi biyu, na farko shi ne, zaben cike gurbi wanda aka samu sakamakon mutuwa ko ajiye aiki ga ‘yan majalisun tarayya da na jiha, inda a zaben zai guda a mazabar ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma ‘yan majalisar wakilai a jihohi uku. Sannan ya ce zaben kashi na biyu kuma za a gudanar da shi ne sakamakon hukuncin kotu.

Idan za a iya tunawa an gudanar da ire-iren wannan ganawa da shugabannin jam’iyyun siyasa a watan da ya gabata, shugaban INEC ya ce a baya an shirya za a gudanar da zaben cike gibi ne a mazabu 35 da ke fadin kasar nan.

Sai dai ya ce a yanzu haka an samu karin mazabu hudu wanda kotun daukaka kara ta umurci hukumar ta gudanar da zabe a mazabar Yabe/Shagari da ke Jihar Sakwato da Madara/Chiade a Jihar Bauchi da kuma Kudan da Kauru/Chawai na Jihar Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Da wannan ne aka samu jimillar mazabu 39 za a gudanar da zaben cike gibi a fadin kasar nan baki daya. Daga cikin adadin, mazabu 9 za a gudanar da sabon zabe ne.

“In ban da guda uku daga cikin mazabun da suka hada da Filato ta Arewa da Arewacin Jos/Bassa a Jihar Filato da Kachia/Kagarko a Jihar Kaduna, duk sauran zaben zai gudana ne a akwatunan zabe kalilan. A wasu wuraren kuma, akwatin zabe guda daya ne kawai za a gudanar da zaben.

“Babban aikin kwamitin samar da tsaro shi ne, tabbatar da an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana. Bisa wannan dalilin ne, hukunar ta riga ta sanar da cewa rundunar ‘yansandar Nijeriya ce za ta jagoranci al’amuran tsaro a lokacin zabe a dukkanin mazabu da ke fadin kasar nan.

“Mun fitar da adadin yawan masu kada kuri’a da suka amshi katin zabe a dukkanin rumfunan zabe da ke fadin kasar nan.

“Duka bayanan da muka yi a baya su ne muka sake maimaitawa a wannan ganawa da mambobin kwamitin samar da tsaro. Sannan za mu saka dukkan bayanan a shafukan sada zumanta na hukumarmu bayan wannan ganawa saboda fadakar da mutane.

“A matsayinmu na hukumomin tsaro, hakkinku ne ku tsare yankunan da za a gudanar da zaben domin ba mu damar jibge jami’anmu da kayayyakin zabe da tsare masu saka ido ciki har ma da ‘yan jarida da wakilan jam’iyyu da kuma ‘yan takara. Idan har ba a samu tsaro ba a mazabun, ba za mu iya gudanar da sahihin zabe ba.

“Bisa abubuwan da suka gabata a baya, zaben cike gurbi yana da matsaloli masu tarin yawa. Za mu mayar da hankali wajen rage lamarin a bangaren wasu ‘yan takara da kuma magoya bayansu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Zargi ‘Yan Siyasa Da Hannu A Haddasa Rikice-rikicen Zabe

Next Post

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

8 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
INEC

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.