• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kalilan da zaben Gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi a ranar Asabar mai zuwa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta umarci kwamishinan zabe (REC) da ke kula da Jihar Sokoto, Dakta Nura Ali, da ya tattara komatsansa ya fice tare da tsame hannunsa daga harkokin hukumar.

Haka nan kuma, tunin aka maye gurbinsa da sakataren gudanarwa ta hukumar a jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa kuma hakan ya fara aiki ne nan take ba tare da bata wani lokaci ba.

  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano
  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Wannan matakin na kunshe ne ta cikin wasikar daga Shalkwatar hukumar da aka aike jihar Sokoto da shi dauke da sanya hannun sakataren hukumar zabe ta kasa, Rose Oriaran-Anthony, mai dauke da kwanan wata 6 ga watan Maris 2023.

Sanarwar mai lambar alama: INEC/SCE/442/V.II, na cewa, “Ana sanar da kai (Dakta Nura Ali), kwamishinan zabe a jihar Sokoto (REC) cewa hukumar INEC ta cimma matsayar umartarka da ka gaggauta ficewa da yin nesa daga ofishin hukumar da ke jihar Sokoto cikin gaggawa har zuwa mataki na gaba”.

“An umarci Sakataren Gudanarwa da ta amshi ragamar kula da hukumar INEC a jihar Sokoto kuma hakan ya fara aiki ne nan take.”

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

A wasikun da wakilinmu ya ci karo da su da dama, sun nanata umarnin da aka bai wa sakataren gudanarwa Hauwa Aliyu Kangiwa da ta karbi cikakken ikon tafiyar da hukumar zabe a jihar Sokoto nan take har zuwa lokacin da hukumar INEC za ta fitar da wani sanarwar ko umarni daban.

Wasikar ta kuma umurce Hauwa da ta da ta tuntubi babban kwamishinansa ido na kasa, Farfesa Muhammad Sani Kaita, domin samun karin haske idan ta na bukatar hakan.

LEADERSHIP ta tuna cewa a ranar Asabar din da ta gabata ne INEC ta sanar da cewa za a haramtawa duk wani ma’aikacin wucin gadi na hukumar muddin aka samu da sakaci da kauce wa ka’idar aiki a lokacin zaben shugaban kasa inda za a haramta masa shiga ko yin aiki a zaben Gwamnoni da ke tafe


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKwamishinan ZabeSakkwato
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: ‘Yan Sanda Za Su Hukunta Masu Yada Labaran Karya A Legas

Next Post

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Related

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

2 weeks ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 weeks ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

4 weeks ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

1 month ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

2 months ago
Next Post
Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam'iyya Ba -LP

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.