• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
3 years ago
INEC

Kwanaki kalilan da zaben Gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi a ranar Asabar mai zuwa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta umarci kwamishinan zabe (REC) da ke kula da Jihar Sokoto, Dakta Nura Ali, da ya tattara komatsansa ya fice tare da tsame hannunsa daga harkokin hukumar.

Haka nan kuma, tunin aka maye gurbinsa da sakataren gudanarwa ta hukumar a jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa kuma hakan ya fara aiki ne nan take ba tare da bata wani lokaci ba.

  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano
  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Wannan matakin na kunshe ne ta cikin wasikar daga Shalkwatar hukumar da aka aike jihar Sokoto da shi dauke da sanya hannun sakataren hukumar zabe ta kasa, Rose Oriaran-Anthony, mai dauke da kwanan wata 6 ga watan Maris 2023.

Sanarwar mai lambar alama: INEC/SCE/442/V.II, na cewa, “Ana sanar da kai (Dakta Nura Ali), kwamishinan zabe a jihar Sokoto (REC) cewa hukumar INEC ta cimma matsayar umartarka da ka gaggauta ficewa da yin nesa daga ofishin hukumar da ke jihar Sokoto cikin gaggawa har zuwa mataki na gaba”.

“An umarci Sakataren Gudanarwa da ta amshi ragamar kula da hukumar INEC a jihar Sokoto kuma hakan ya fara aiki ne nan take.”

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

A wasikun da wakilinmu ya ci karo da su da dama, sun nanata umarnin da aka bai wa sakataren gudanarwa Hauwa Aliyu Kangiwa da ta karbi cikakken ikon tafiyar da hukumar zabe a jihar Sokoto nan take har zuwa lokacin da hukumar INEC za ta fitar da wani sanarwar ko umarni daban.

Wasikar ta kuma umurce Hauwa da ta da ta tuntubi babban kwamishinansa ido na kasa, Farfesa Muhammad Sani Kaita, domin samun karin haske idan ta na bukatar hakan.

LEADERSHIP ta tuna cewa a ranar Asabar din da ta gabata ne INEC ta sanar da cewa za a haramtawa duk wani ma’aikacin wucin gadi na hukumar muddin aka samu da sakaci da kauce wa ka’idar aiki a lokacin zaben shugaban kasa inda za a haramta masa shiga ko yin aiki a zaben Gwamnoni da ke tafe

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Next Post
Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam'iyya Ba -LP

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.