• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kalilan da zaben Gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi a ranar Asabar mai zuwa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta umarci kwamishinan zabe (REC) da ke kula da Jihar Sokoto, Dakta Nura Ali, da ya tattara komatsansa ya fice tare da tsame hannunsa daga harkokin hukumar.

Haka nan kuma, tunin aka maye gurbinsa da sakataren gudanarwa ta hukumar a jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa kuma hakan ya fara aiki ne nan take ba tare da bata wani lokaci ba.

  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano
  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Wannan matakin na kunshe ne ta cikin wasikar daga Shalkwatar hukumar da aka aike jihar Sokoto da shi dauke da sanya hannun sakataren hukumar zabe ta kasa, Rose Oriaran-Anthony, mai dauke da kwanan wata 6 ga watan Maris 2023.

Sanarwar mai lambar alama: INEC/SCE/442/V.II, na cewa, “Ana sanar da kai (Dakta Nura Ali), kwamishinan zabe a jihar Sokoto (REC) cewa hukumar INEC ta cimma matsayar umartarka da ka gaggauta ficewa da yin nesa daga ofishin hukumar da ke jihar Sokoto cikin gaggawa har zuwa mataki na gaba”.

“An umarci Sakataren Gudanarwa da ta amshi ragamar kula da hukumar INEC a jihar Sokoto kuma hakan ya fara aiki ne nan take.”

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

A wasikun da wakilinmu ya ci karo da su da dama, sun nanata umarnin da aka bai wa sakataren gudanarwa Hauwa Aliyu Kangiwa da ta karbi cikakken ikon tafiyar da hukumar zabe a jihar Sokoto nan take har zuwa lokacin da hukumar INEC za ta fitar da wani sanarwar ko umarni daban.

Wasikar ta kuma umurce Hauwa da ta da ta tuntubi babban kwamishinansa ido na kasa, Farfesa Muhammad Sani Kaita, domin samun karin haske idan ta na bukatar hakan.

LEADERSHIP ta tuna cewa a ranar Asabar din da ta gabata ne INEC ta sanar da cewa za a haramtawa duk wani ma’aikacin wucin gadi na hukumar muddin aka samu da sakaci da kauce wa ka’idar aiki a lokacin zaben shugaban kasa inda za a haramta masa shiga ko yin aiki a zaben Gwamnoni da ke tafe


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKwamishinan ZabeSakkwato
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: ‘Yan Sanda Za Su Hukunta Masu Yada Labaran Karya A Legas

Next Post

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Related

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

23 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

24 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

1 day ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

1 day ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

3 days ago
Next Post
Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam'iyya Ba -LP

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.