ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Kori Kwamishinan Zaben Sakkwato Gabanin Shiga Zaben Gwamnoni

by Khalid Idris Doya
3 years ago
INEC

Kwanaki kalilan da zaben Gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi a ranar Asabar mai zuwa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta umarci kwamishinan zabe (REC) da ke kula da Jihar Sokoto, Dakta Nura Ali, da ya tattara komatsansa ya fice tare da tsame hannunsa daga harkokin hukumar.

Haka nan kuma, tunin aka maye gurbinsa da sakataren gudanarwa ta hukumar a jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa kuma hakan ya fara aiki ne nan take ba tare da bata wani lokaci ba.

  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano
  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Wannan matakin na kunshe ne ta cikin wasikar daga Shalkwatar hukumar da aka aike jihar Sokoto da shi dauke da sanya hannun sakataren hukumar zabe ta kasa, Rose Oriaran-Anthony, mai dauke da kwanan wata 6 ga watan Maris 2023.

ADVERTISEMENT

Sanarwar mai lambar alama: INEC/SCE/442/V.II, na cewa, “Ana sanar da kai (Dakta Nura Ali), kwamishinan zabe a jihar Sokoto (REC) cewa hukumar INEC ta cimma matsayar umartarka da ka gaggauta ficewa da yin nesa daga ofishin hukumar da ke jihar Sokoto cikin gaggawa har zuwa mataki na gaba”.

“An umarci Sakataren Gudanarwa da ta amshi ragamar kula da hukumar INEC a jihar Sokoto kuma hakan ya fara aiki ne nan take.”

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

A wasikun da wakilinmu ya ci karo da su da dama, sun nanata umarnin da aka bai wa sakataren gudanarwa Hauwa Aliyu Kangiwa da ta karbi cikakken ikon tafiyar da hukumar zabe a jihar Sokoto nan take har zuwa lokacin da hukumar INEC za ta fitar da wani sanarwar ko umarni daban.

Wasikar ta kuma umurce Hauwa da ta da ta tuntubi babban kwamishinansa ido na kasa, Farfesa Muhammad Sani Kaita, domin samun karin haske idan ta na bukatar hakan.

LEADERSHIP ta tuna cewa a ranar Asabar din da ta gabata ne INEC ta sanar da cewa za a haramtawa duk wani ma’aikacin wucin gadi na hukumar muddin aka samu da sakaci da kauce wa ka’idar aiki a lokacin zaben shugaban kasa inda za a haramta masa shiga ko yin aiki a zaben Gwamnoni da ke tafe

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

December 16, 2025
Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka
Da ɗumi-ɗuminsa

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

December 9, 2025
An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa

December 9, 2025
Next Post
Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam’iyya Ba -LP

Zaben Gwamnoni: Ba Mu Yi Hadaka Da Kowace Jam'iyya Ba -LP

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.