ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

by Leadership Hausa
2 months ago
Sule

Ya dawo gida daga Amurka ba, amma ba a matsayin wanda ya yi ritaya ba, illa kawai don sake fasalin jihar baki-ɗaya, musamman ta fuskar inganta masana’antu.

Daga Gudi Zuwa Ɗaukaka

A ƙauyen Gudi, inda suke da al’adu daban-daban tare da zaman lafiya, a nan Abdullahi Sule ya fara koyon horon aiki.

ADVERTISEMENT

An haife shi a ranar 26 ga Disambar 1959, barin garinsu da ke Nasarawa zuwa yunƙurin kawo sauyi a jihar, na da alaƙa da kyakkyawar manufa da kuma hangen nesa.

  • Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa
  • ‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Sai ga shi yau, yaron da fito daga Gudi ya kasance a matsayin mai tsara yadda za a inganta masana’antu a Jihar Nasarawa, kuma shugaba gogagge, wanda ya zagaya duniya tare da sanin matsalolin gida, wannan ne yasa labarinsa ya yi fice a Arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Injiniya Mai Matuƙar Hangen Nesa

Tun kafin ya shiga siyasa, Sule ya kasance mutum mai gaskiya da aiki tuƙuru. Bayan kammala karatun digirinsa na farko da na biyu a Amurka, duk a fannin Injiniyarin da Fasahar Masana’antu, B.Sc da M.Sc daga Jami’ar Jihar Indiana, ya kuma haɓaka ƙwarewarsa a manyan kamfanonin injiniya na Amurka, daga Dril-Ƙuip zuwa Kamfanin Osyka, inda ya zama daraktan ci gaban kasuwanci na Afirka da Gabas ta Tsakiya.

Lokacin da ya dawo Nijeriya, a shekara ta 2000, ba kawai da takaddun shaida ya dawo ba, ya dawo ne da cikakkiyar ƙwarewa. Shi ne ya kafa kamfanin mai na Sadiƙ Petroleum, ya jagoranci tafiyar da kamfanin na ‘African Petroleum Plc’, sannan ya zama Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Siga na Dangote, inda ya yi ƙaurin suna wajen inganci da ƙirƙire-ƙirƙire.

Waɗannan abubuwa, sun ne suka zama ginshiƙan manufar siyasarsa, wajen tafiyar da Jihar Nasarawa; musamman ta fuskar kasuwanci.

Hange Da Dabarunsa Na Aiki

Lokacin da ya kama aiki a matsayin gwamna, Gwamna Sule ya zo da wani shiri, mai suna ‘Nassarawa Economic Deɓelopment Strategy (NEDS)’.

Wannan ita ce cikakkiyar taswirar ci gaban jihar ta farko, wadda aka gina ta a kan masana’antu da samar da ababen more rayuwa, ci gaban kasuwancin al’umma da kuma shugabanci na gari.

NEDS, ta sake fasalin yanayin tattalin arziƙin Jihar Nasarawa, daga yankin noma zuwa wani yanki na saka hannun jari.

A ƙarƙashin jagorancinsa, jihar ta jawo hankalin masu zuba jari na gida da waje a masana’antu, ma’adanai, wutar lantarki da noma, inda ya mayar da Jihar Nasarawa matsayin cibiyar masana’antu ta Nijeriya.

Hasashensa na tattalin arziƙi, na da inganci kamar yadda yake da buri: mayar da fa’idar da jihar ke da ita cikin ma’adanai masu ƙarfi, kusanci da Abuja da yawan sanya matasa yin gasa a tsakaninsu.

Masana’antu A Matsayin Ginshiƙin Ci Gaba

Tsarin mulki na Gwamna Sule, yana ɗaukar masana’antu a matsayin abubuwan more rayuwa. Tun daga fafutukar ci gaban birane da gwamnatinsa ta yi na gina manyan titunan birane zuwa wuraren shaƙatawa na masana’antu a ƙauyen Nasarawa, zuwa ayyukan makamashin da za a sabunta, jihar na ci gaba da zama babbar wata hanya ta zuba jari.

Ta hanyar haɗin gwiwa da gangan, Jihar Nasarawa ta jawo hankalin kamfanoni, domin samar da siminti, ma’adanan lithium, sarrafa ethanol, samar da ayyukan yi, kuɗaɗen shiga da sauransu.

Haɗin gwiwar da jihar ke yi da Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), kan amfani da iskar gas da kafa aikin haƙo mai da iskar Gas na Nasarawa, ya nuna ƙwaƙƙwaran matakai na samun wadatar makamashi da matuƙar ƙima.

Ayyukan Ababen More Rayuwa Da Sha’anin Mulkin

Yunƙurin sabunta ababen more rayuwa na Gwamna Sule, abu ne da ya samo asali. Hanyoyi, Makarantu da asibitoci, sun bazu a ko’ina cikin ƙananan hukumomi, don tabbatar da ganin cewa; ba a bar al’umma a baya ba.

Bayan ayyuka na zahiri, ana ayyana mulkinsa ta hanyar bayyana gaskiya, haɗin gwiwar jama’a da sake fasalin hukumomi.

Gwamnatinsa ta ɓullo da tsarin gudanar da filaye a zamanance, gyare-gyaren haraji wanda ya dace da zuba jari da tsarin PPP, wanda ke taimakawa wajen sauƙaƙa kasuwanci da samun bunƙasarsa.

Yana kuma faɗaɗa bayar da damar ilimi da sana’o’i, domin gina tushen jarin Ɗan’adam, wanda zai ci gaba da ingiza ci gaban masana’antun jihar.

Masanin Makamar Aiki A Mulki

Waɗanda suka san shi, sun bayyana Injiniya Sule ba a matsayin ɗan siyasa ba, illa a matsayin masanin makamar aiki, gogagge, mai kuma tarin ƙwarewa. Ya kawo wa gwamnatin tasa sahihancin injiniya da kuma hazaƙar da ya samu a matsayin manaja.

Tarihinsa- daga Kamfanin ‘Jos Steel Rolling Company’ zuwa na ‘African Petroleum’, sun ba shi ƙwarewar jagoranci da kuma tawali’u, musamman wajen saurarar mutane dangane matsalolinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan'uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.