• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IPC Ta Yi Tir Da Muzguna Wa ‘Yan Jarida Yayin Daukan Rahoton Shari’ar Kujerar Gwamna A Kano

by Khalid Idris Doya
2 years ago
IPC

Cibiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa (IPC) da cibiyar kare hakkin ‘yan jarida (I-CSPJ) da ke da reshe a jihar Legas ta yi allawadai dangane da yadda wasu jami’an ‘yansanda suka muzguna ma wasu ‘yan jarida a lokacin da suke bakin aikinsu na dauko rahoton shari’ar kujerar gwamnan Kano da aka gudanar a ranar Laraba.

Hakan na kunshe ne acikin wata sanarwa da ta fito mai dauke da sa hannun jami’in I-CSPJ Melody Akinjiyan wadda aka aike wa ‘yan jaridu.

  • NUJ Ta Yi Kira Ga Jami’an Tsaro Da Su Gaggauta Zakulo Wadanda Suka Yi Wa Danjarida Kisan Gilla A Zamfara

Sanarwar ta bayyana sunayen ‘yan jaridar da aka kai wa harin da Salim Umar Ibrahim na Daily Trust da kuma wakilin BBC Hausa, Zahraddeen Lawal.

Rahoto da ya fito daga bakin Salim Ibrahim na gidan jaridar Daily Trust ya bayyana cewa, ‘’’Yansandan da ke bakin aiki sun bukaci ‘yan jaridan da su yi nesa da harabar kotun kimanin nisan mita 10, ana cikin haka ne kawai sai wasu daga cikin ‘yansandan suka dirar wa ‘yan jarida wai suna daukar hoto.

“Sannan kuma suka bi ma’aikacin BBC, inda suke kokarin kwace masa wayarsa, wasu kuma daga cikinsu suka farwa Salim Ibrahim na jaridar Daily Trust inda suka karbe masa wayarsa ta karfin tsiya, tare da lalata masa wayar,” cewar rahoton.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Babban Darakta IPC, Mista Lanre Arogundade ya ce, “Harin ba gaira ba dalili da ake kai wa ‘yan jarida a bakin aikinsu babbar kalubale ne da wukakanta dimokuradiyyar mu kuma a wurin mu babbar barazana ce ga ‘yancin ‘yan jarida. Irin wannan hukuncin ya saba wa hakkokin ‘yan jarida.”

Sannan cibiyar ta bukaci rundunar ‘yansandan Nijeriya da su bi a hankali game da irin matakan da suke dauka a kan ‘yan jarida, domin hakan na iya haifar da tsoro ga ‘yan jarida ya yin gudanar da ayyukan su.

Melody Akinjiyan ta kuma ce cibiyar ta yi kira ga kwamishinan ‘yansandan jihar Kano da ya dauki kwakkwaran matakai da suka dace don ganin an hukunta wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da tsaurara matakai wajen ganin an biya wadanda aka ciwa zarafi diyya.

Ta kuma yi kira ga jami’an ‘yansanda da su kasance masu ba wa ‘yan jarida hadin kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.