ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Gobara

Wata tanka ɗauke da fetur (PMS) ta kife a ranar Lahadi a jihar Legas inda nan take ta kama da wuta. Gobarar ta bazu cikin sauri, ta laƙume aƙalla manyan motoci guda huɗu da aka ajiye a wajen Iyana-Isolo zuwa Oshodi.

Daraktan sashin hulɗa da Jama’a na hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas (LASTMA), Taofiq Adebayo, ya bayyana cewa binciken farko ya nuna gudun wuce gona da iri ne ya sa direban ya rasa iko da motar, abin da ya haifar da mummunar haɗarin.

  • A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
  • Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

Cikin gaggawa jami’an LASTMA, tare da haɗin gwiwar ma’aikatan kashe gobara da jam’ian ƴansanda daga Aswani, da Ilasa da Mushin, da ma jami’an tsaro na unguwanni ne suka yi aiki tukuru wajen shawo kan gobarar kafin ta girmama.

ADVERTISEMENT

Babban Daraktan LASTMA, Olalekan Bakare-Oki, ya tabbatar da cewa babu asarar rai, yana mai jaddada cewa hakan ya faru ne saboda saurin rufe hanyar da kuma dakatar da motoci daga Ilasa zuwa Oshodi. Ya gargadi direbobin manyan motoci da tankoki su kiyaye gudun wuce sa’a domin kare rayuka da dukiyoyi.

Ya kuma buƙaci jama’a da su rika amfani da layin waya kyauta na LASTMA wajen sanar da kowanne irin hatsari ko matsalar hanya, domin hukumar ta ci gaba da kare lafiyar al’umma da kuma tabbatar da tsari a hanyoyin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Gobara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq
  • Abubakar Sulaiman
    Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Labarai

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

June 18, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano
Manyan Labarai

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

June 18, 2026
Next Post
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

June 18, 2026
Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

June 18, 2026
Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

June 18, 2026
Tinubu

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026
Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

June 18, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

June 18, 2026
Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

June 18, 2026
Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

June 18, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.