ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ISWAP Ta Hallaka Kwamandan Boko Haram A Sambisa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Sambisa

Mayakan kungiyar ISWAP sun hallaka kwamandan Boko Haram mai shugabantar kungiyar a Sambisa da Gwoza, Ali Gana Alhaji Ali a dajin Gwoza da ke karamar hukumar Gwoza a jihar Borno.

Majiyar tsaro ta shaida wa Daily Trust cewa, Ali na daya daga cikin manyan shugabannin kungiyar Boko Haram, an kashe shi ne a wani farmakin da mayakan ISWAP suka kaddamar a kan ‘ya’yan kungiyar a ranar Lahadi.

  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 41 Yayin Da Boko Haram Da ISWAP Suka Bai Wa Hammata Isla A Borno
  • ‘Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

“Shi ne mataimakin marigayi Ali Ndulde, baya ga Shekau, babu wani mutum da ya kashe mutane kamarsa a dukkanin dajin Sambisa da Bayan Dutsen Gwoza.

ADVERTISEMENT

“Shahararren makashi ne. Aikin ta’addancinsa a yankin Gwoza ya sanya al’ummar kauyuka, manoma da mazauna yankin Pulka, Bankin, Bama da Gwoza Mubi cikin tsananin fargaba da tsoro da zullumi.

“Ba su daukan fursuna balle ma su ajiyesu, suna yankan rago ga mutane a kusan kowane sati a gonakansu. Tabbas al’ummar Gwoza za su yi murna da maraba bisa jin labarin mutuwarsa,” inji majiyar.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Wannan ci gaban na zuwa ne bayan shekaru biyu da babban kwamandan Boko Haram, Abubakar Shekau, ya tarwatsa kansa da kansa a wani mummunar gumurzu da suka yi da mayakan ISWAP a watan Mayun 2021.

A makon da ya gabata ne, dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gwoza, Damboa da Chibok a majalisar wakilai ta tarayya, Usman Ahmed Jaha, ya nuna damuwarsa dangane da kisan manoma 10 a cikin kwanaki 10 a yankin Goza.

Ya yi korafin cewa ana kashe manoma kusan kullum a yankin a yayin da suke kokarin ciro amfanin gonakansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Wannan Takarda Ta Nuna Burin Kasar Sin A Fannin Hulda Da Sauran Kasashe

Wannan Takarda Ta Nuna Burin Kasar Sin A Fannin Hulda Da Sauran Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.