• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayena Ba Su Kalubalanci Shigata Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara

by Rabi'at Sidi Bala
2 months ago
in Nishadi
0
Iyayena Ba Su Kalubalanci Shigata Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitacciyar Jarumar fina-finan hausa dake masana’antar kannywood HADIZA MUHAMMAD wadda aka fi sani da HADIZA KABARA, ta bayyana irin kalubalen da suka fuskanta sama da shekara ashirin kafin shigarsu cikin masana’antar Kannywood, har ma da bayan shigar su, ta kuma yi bayani dangane da wasu abubuwan da suka shafi rayuwarta da kuma sana’arta ta fim. Ga dai tattaunawar tare da wakikiyarmu RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko za ki fadawa masu karatu cikakken sunanki, tare da sunan da aka fi saninki da shi.
Sunana Hadiza Muhammad Sani, wadda aka fi sani da Hadiza Kabara, a yanzu kuma an fi sani na da Lantana ko Hauwan dan Badamasi.

Masu karatu za su so su ji dan takaitaccen tarihinki.
Ni haifaffiyar Kano ce, an haife ni a unguwar Yakasai wajen masallacin Jalli, daga nan iyayena aiki ya dawo da su Chalawa wajen Fanshekara. Na yi makarantar firamare a ‘Panshekara Special Primary School’, daga nan na zo na yi makarantar sakandare a ‘Gov. Girls Arabic Secondary School’ Babura. A yanzu ba ni da aure ina tare da yarana guda biyu, wannan shi ne a takaice.

Wanne rawa kike takawa a cikin masana’antar Kannywood?

hadiza kabara
A yanzu dai ina taka rawa kala-kala, ko kuma na ce yanzu tunda girma ya zo mun manyanta, kin san ‘industry’ din da sanda muke ciki mu ne yaran a shekaru can kusan goma sha da suka wuce, ko na ce ashirin ma, mu ne yara. Toh! kuma mu ne iyayen yaran, akwai kakanninmu yanzu, yanzu mu ne iyaye, ina taka rawa matsayin uwa.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d

Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty

Bangaren shirya fim ko makamancin haka fa?
Yanzu dai na fi karfi a kan matsayin Jaruma, ni Jaruma ce yanzu.

Me ya ja hankalinki har kika tsunduma harkar fim?
Abin da ya ja hankalina shekaru masu yawa akwai wani tsohon fim din sarauniya wato Allura da Zare, dan sarauniyar na biyu ce. Akwai sarauniya ta gwammaja, akwai wani fim dinsu na Allura da Zare, ina kallo-ina kallo, bayan na gama ‘Secondary School’, sai na zo na shiga ‘Industry’. Toh! akwai wani dan uwana shi yana harkar, na ma ganshi a fim din sai na yi masa magana, ya ce; “Toh! ba matsala tunda iyayenki suka yarda to za a iya kai ki”. Toh! wannan fim din ya yi matukar birge ni, kuma na ga an fadakar shiyasa na ga bari na shiga, da yardar Allah dana fada kuma sai ba samu yadda nake so.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance, kamar yadda za ki ga wasu da kuka da shigar?
Mu dai lokacin da muka shiga ‘Industry’ din a lokacin aka buga gwagwarmaya, ba ma ‘yan wasan sosai a lokacin, musamman ma bangaren mata. Lokacin da muka zo ‘industry’ din ma yawanci Maza ne ma suke dan shigar Mata, mu lokacin ba mu da yawa ba mu fi ‘yan tsiraui ba, ba mu fi mu hudu ko biyar ba. Mun zo mun samu Fati Muhammad da Allah ya ji kan rai Hauwa Ali Dodo, sai wata Hasiya Aya, lokacin ma sai dai a ce su ne ‘yan matan. Kin san Hauwa Ali Dodo ba rol din da ba ta bugawa Allah ya ji kan rai. Toh! Sanda muka zo kafin ma a yarda a fara samu a fim din ma mun dan sha wuya, sai mun je ‘location’ din ma sai a ce kai mu tafi gida mun yi kankanta, ko kuma dai “iyayenku sun yarda?”. Toh! Mun samu kalubale kala-kala, kafin Allah ya lamunce mana, yanzu ga shi nan muna cikin harkar da yardar Allah.

hadiza kabara

Lokacin da kika fara cin karo da kalubalen cikin masana’antar ba ki ji kamar ki hakura ba?
Ai duk wata harka da ba za ka hadu da kalubale ba, toh! ka san ba nasara a cikinta, duk abin da ba za ka hadu da kalubale ba, kai ma ka kuka da kanka ka san ba nasara, gwara ka janye ka sake sana’a. Mun fuskanci kalubale kala-kala, amma wannan abun bai sa mun ja baya ba, jajircewa muka yi, amma kalubale mun hadu da shi kala-kala, amma kuma duk da hakan ban taba jin zan fita daga masana’antar ba, sabida ina son abun, ina son aikin kuma Allah ya taimake ni.

Bayan da kika yi nasarar samun shiga cikin masana’antar ya kika ji a lokacin?
A lokacin dana samu kaina a cikin masana’anta ba ni da wayo, irin abin da na ji ma ba zan tantance ba yanzu gaskiya, saboda abin ya dade sosai.

Bayan da kika shiga cikin masana’antar, ko akwai wani kalubalen da kika kara fuskanta?
Kalubale na fada a baya na fuskata kala-kala, wasu ma ni ba zan iya tuna su ba, wannan sirri ne na barwa zuciyata.

Toh! ya batun iyaye fa, lokacin da kika sanar musu kina son shiga, shin kin samu wani kalubale daga gare su?
A’a! Kwata-kwata ni ban samu ba, ban samu kalubale ba wajen iyayena, addu’a suka bini da shi, kuma shi ne na tabbatar addu’ar ce take ta bi na. Ka san ‘by the time’ din da danka ya zo maka da abu ka nuna ina! aka hau wani tashin hankali da sauransu, idan har iyaye ba su sa maka hannu ba, ko ba su yi maka addu’a ba toh ka hakura da abun. Toh! ni sa Allah ya taimake ni adduarsu’a suka bi ni da shi.

Daga lokacin da kika fara kawo iyanzu, za ki yi kamar shekara nawa?
Daga lokacin dana fara fim kawo iyanzu, zan yi kamar shekara ashirin ko ashirin da wani abu.

Da wanne fim kika fara, kuma wanne rawa kika taka cikin fim din?
Na fara da wani fim ne me suna ‘MALAM KARKATA’, sau biyu na fito a fim din, ni har yanzun ma ban taba ganin fim din ba, bai fita ba. Daga baya aka zo aka yi mun wani fim ‘HUKUNCI’, aka zo aka yi mun ‘DABI’A’. Wannan DABI’A shi ne dai kowa ya sanni da shi, amma fim dina na farko shi ne; ‘MALAM KARKATA’. An debo irin wanda suka zo wajen boka neman taimako, toh fita biyu nayi a wannan fim din. Shi kuma HUKUNCI ni ce me jan fim din, dana fito a budurwa da saurayi.

hadiza kabara

Ko za ki iya tuna yawan adadin fina-finan da kika yi?
Gaskiya ba wani abu da zan iya tunawa wallahi, na san dai kawai na yi da yawa yadda ba ma za su misaltu ba.
Za mu ci gaba

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Kasar Sin Kan Ababen More Rayuwa Ya Gaggauta Ci Gaban Nahiyar Afrika 

Next Post

Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar ‘Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

Related

A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d
Nishadi

A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d

2 days ago
Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty
Nishadi

Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty

2 days ago
Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog
Nishadi

Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

2 days ago
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King
Nishadi

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

4 days ago
Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya
Nishadi

Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya

3 weeks ago
Nishadantar Da Mutane Ya Sa Na Shiga Wasan Barkwanci –Yusuf Abubakar
Nishadi

Nishadantar Da Mutane Ya Sa Na Shiga Wasan Barkwanci –Yusuf Abubakar

1 month ago
Next Post
Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar ‘Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar 'Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

March 27, 2023
Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.