ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayena Ba Su Kalubalanci Shigata Harkar Fim Ba —Hadiza Kabara

by Rabi'at Sidi Bala
4 years ago
hadiza kabara

Fitacciyar Jarumar fina-finan hausa dake masana’antar kannywood HADIZA MUHAMMAD wadda aka fi sani da HADIZA KABARA, ta bayyana irin kalubalen da suka fuskanta sama da shekara ashirin kafin shigarsu cikin masana’antar Kannywood, har ma da bayan shigar su, ta kuma yi bayani dangane da wasu abubuwan da suka shafi rayuwarta da kuma sana’arta ta fim. Ga dai tattaunawar tare da wakikiyarmu RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko za ki fadawa masu karatu cikakken sunanki, tare da sunan da aka fi saninki da shi.
Sunana Hadiza Muhammad Sani, wadda aka fi sani da Hadiza Kabara, a yanzu kuma an fi sani na da Lantana ko Hauwan dan Badamasi.

Masu karatu za su so su ji dan takaitaccen tarihinki.
Ni haifaffiyar Kano ce, an haife ni a unguwar Yakasai wajen masallacin Jalli, daga nan iyayena aiki ya dawo da su Chalawa wajen Fanshekara. Na yi makarantar firamare a ‘Panshekara Special Primary School’, daga nan na zo na yi makarantar sakandare a ‘Gov. Girls Arabic Secondary School’ Babura. A yanzu ba ni da aure ina tare da yarana guda biyu, wannan shi ne a takaice.

ADVERTISEMENT

Wanne rawa kike takawa a cikin masana’antar Kannywood?

hadiza kabara
A yanzu dai ina taka rawa kala-kala, ko kuma na ce yanzu tunda girma ya zo mun manyanta, kin san ‘industry’ din da sanda muke ciki mu ne yaran a shekaru can kusan goma sha da suka wuce, ko na ce ashirin ma, mu ne yara. Toh! kuma mu ne iyayen yaran, akwai kakanninmu yanzu, yanzu mu ne iyaye, ina taka rawa matsayin uwa.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Bangaren shirya fim ko makamancin haka fa?
Yanzu dai na fi karfi a kan matsayin Jaruma, ni Jaruma ce yanzu.

Me ya ja hankalinki har kika tsunduma harkar fim?
Abin da ya ja hankalina shekaru masu yawa akwai wani tsohon fim din sarauniya wato Allura da Zare, dan sarauniyar na biyu ce. Akwai sarauniya ta gwammaja, akwai wani fim dinsu na Allura da Zare, ina kallo-ina kallo, bayan na gama ‘Secondary School’, sai na zo na shiga ‘Industry’. Toh! akwai wani dan uwana shi yana harkar, na ma ganshi a fim din sai na yi masa magana, ya ce; “Toh! ba matsala tunda iyayenki suka yarda to za a iya kai ki”. Toh! wannan fim din ya yi matukar birge ni, kuma na ga an fadakar shiyasa na ga bari na shiga, da yardar Allah dana fada kuma sai ba samu yadda nake so.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance, kamar yadda za ki ga wasu da kuka da shigar?
Mu dai lokacin da muka shiga ‘Industry’ din a lokacin aka buga gwagwarmaya, ba ma ‘yan wasan sosai a lokacin, musamman ma bangaren mata. Lokacin da muka zo ‘industry’ din ma yawanci Maza ne ma suke dan shigar Mata, mu lokacin ba mu da yawa ba mu fi ‘yan tsiraui ba, ba mu fi mu hudu ko biyar ba. Mun zo mun samu Fati Muhammad da Allah ya ji kan rai Hauwa Ali Dodo, sai wata Hasiya Aya, lokacin ma sai dai a ce su ne ‘yan matan. Kin san Hauwa Ali Dodo ba rol din da ba ta bugawa Allah ya ji kan rai. Toh! Sanda muka zo kafin ma a yarda a fara samu a fim din ma mun dan sha wuya, sai mun je ‘location’ din ma sai a ce kai mu tafi gida mun yi kankanta, ko kuma dai “iyayenku sun yarda?”. Toh! Mun samu kalubale kala-kala, kafin Allah ya lamunce mana, yanzu ga shi nan muna cikin harkar da yardar Allah.

hadiza kabara

Lokacin da kika fara cin karo da kalubalen cikin masana’antar ba ki ji kamar ki hakura ba?
Ai duk wata harka da ba za ka hadu da kalubale ba, toh! ka san ba nasara a cikinta, duk abin da ba za ka hadu da kalubale ba, kai ma ka kuka da kanka ka san ba nasara, gwara ka janye ka sake sana’a. Mun fuskanci kalubale kala-kala, amma wannan abun bai sa mun ja baya ba, jajircewa muka yi, amma kalubale mun hadu da shi kala-kala, amma kuma duk da hakan ban taba jin zan fita daga masana’antar ba, sabida ina son abun, ina son aikin kuma Allah ya taimake ni.

Bayan da kika yi nasarar samun shiga cikin masana’antar ya kika ji a lokacin?
A lokacin dana samu kaina a cikin masana’anta ba ni da wayo, irin abin da na ji ma ba zan tantance ba yanzu gaskiya, saboda abin ya dade sosai.

Bayan da kika shiga cikin masana’antar, ko akwai wani kalubalen da kika kara fuskanta?
Kalubale na fada a baya na fuskata kala-kala, wasu ma ni ba zan iya tuna su ba, wannan sirri ne na barwa zuciyata.

Toh! ya batun iyaye fa, lokacin da kika sanar musu kina son shiga, shin kin samu wani kalubale daga gare su?
A’a! Kwata-kwata ni ban samu ba, ban samu kalubale ba wajen iyayena, addu’a suka bini da shi, kuma shi ne na tabbatar addu’ar ce take ta bi na. Ka san ‘by the time’ din da danka ya zo maka da abu ka nuna ina! aka hau wani tashin hankali da sauransu, idan har iyaye ba su sa maka hannu ba, ko ba su yi maka addu’a ba toh ka hakura da abun. Toh! ni sa Allah ya taimake ni adduarsu’a suka bi ni da shi.

Daga lokacin da kika fara kawo iyanzu, za ki yi kamar shekara nawa?
Daga lokacin dana fara fim kawo iyanzu, zan yi kamar shekara ashirin ko ashirin da wani abu.

Da wanne fim kika fara, kuma wanne rawa kika taka cikin fim din?
Na fara da wani fim ne me suna ‘MALAM KARKATA’, sau biyu na fito a fim din, ni har yanzun ma ban taba ganin fim din ba, bai fita ba. Daga baya aka zo aka yi mun wani fim ‘HUKUNCI’, aka zo aka yi mun ‘DABI’A’. Wannan DABI’A shi ne dai kowa ya sanni da shi, amma fim dina na farko shi ne; ‘MALAM KARKATA’. An debo irin wanda suka zo wajen boka neman taimako, toh fita biyu nayi a wannan fim din. Shi kuma HUKUNCI ni ce me jan fim din, dana fito a budurwa da saurayi.

hadiza kabara

Ko za ki iya tuna yawan adadin fina-finan da kika yi?
Gaskiya ba wani abu da zan iya tunawa wallahi, na san dai kawai na yi da yawa yadda ba ma za su misaltu ba.
Za mu ci gaba

hadiza kabara
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
hadiza kabara
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar ‘Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar 'Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina

An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

September 15, 2026
Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

September 15, 2026
Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Bukaci A Nada Kwamitin Watanni 6 Domin Warware Matsalolin Hukumar

Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Bukaci A Nada Kwamitin Watanni 6 Domin Warware Matsalolin Hukumar

September 15, 2026
Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

September 15, 2026
NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

September 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

September 15, 2026
'yansanda

Gargaɗi: ‘Yansanda Sun Gano Shirin Kai Hare-hare A Makarantu Da Wuraren Ibada

September 15, 2026
Majalisar Dinkin Duniya Ta Karbi Samfurin Bincike Da Kasar Sin Ta Gudanar A Duniyar Wata  

Majalisar Dinkin Duniya Ta Karbi Samfurin Bincike Da Kasar Sin Ta Gudanar A Duniyar Wata  

September 15, 2026
Dangote

Dalilin Da Ya Sanya Tsadar Man Fetur Ke Ci Gaba Da Shafar Nijeriya — Dangote

September 15, 2026
Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

September 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.