ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Bangladesh Ya Yaba Wa MAAUN, Ya Buƙaci A Kafa Reshen Jami’ar A Ƙasarsa 

by Bello Hamza and Sulaiman
3 weeks ago
MAAUN

Jakadan Bangladesh a Nijeriya, Mista Miah Mainul Kabir, ya yi kira da a kafa reshen Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) a ƙasar Bangladesh.

 

Mista Mainul Kabir ya bayyana wannan buƙata ne a lokacin da ya ziyarci MAAUN Kano a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa buɗe reshen MAAUN a Bangladesh zai ƙara fito da jami’ar a idon duniya wajen haɓaka ilimi da basirar ƙere-ƙere a matakin ƙasa da ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kano Ta Fara Ɗaukar Matakan Daƙile Dawowar Masu Achaba
  • Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (2)

Jakadan ya yaba wa MAAUN bisa yadda shahararta yake ƙaruwa wajen ingancin karatu da bincike kan ƙirkire-ƙirkire, yana mai cewa jajircewar jami’ar wajen ƙirƙira ta zama abin koyi ga sabbin jami’o’i a faɗin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Jakadan ya kasance a jami’ar ne domin gabatar da lacca mai taken: “Amfani da Ƙwarewar Matasa wajen Tattalin Arziki da Cigaban Zamantakewa.”

 

Laccar wadda Ofishin Jakadancin Bangladesh da ke Abuja tare da haɗin gwiwar MAAUN suka shirya, ta yi nufin ƙarfafa matasa domin gina kyakkyawar makoma ga kansu da ƙasa baki ɗaya.

 

Tun kafin fara laccar, hukumar gudanarwar jami’ar da jakadan Bangladesh da tawagarsa sun yi dogon zama kan fannoni daban-daban na yiwuwar haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da ƙasar Bangladesh.

 

Ya jaddada ƙoƙarin da ofishin jakadancin ke yi na tuntuɓar gwamnatoci, cibiyoyi da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin samar da haɗin gwiwar da za ta haifar da ci gaba mai ma’ana.

 

Daga bisani, an zagaya da Jakadan da tawagarsa wasu muhimman sassa na jami’ar, ciki har da MAAUN Innovation Hub da ke cikin School of Computing, inda ya duba kayan aiki da ake amfani da su a wurin.

 

A jawabinsa na maraba, Shugaban MAAUN, Farfesa (Dr.) Mohammad Israr, ya ce wannan lacca daga jakadan Bangladesh shaida ce ta jajircewar MAAUN wajen gina haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da kuma ƙarfafa matasa.

 

Ya jaddada buƙatar samar wa matasa ƙwarewa, ilimi da damar da ake buƙata domin su taka rawar gani wajen kawo cigaba mai ma’ana.

 

A nasa ɓangaren, Mataimakin Shugaban Jami’ar (ɓangaren gudanarwa), Dr. Habib Awaisu Abubakar, ya yaba wa Ofishin Jakadancin Bangladesh da kuma MAAUN bisa yunƙurin faɗaɗa haɗin gwiwa domin ƙarfafa fannin ilimi da ci gaba.

 

A yayin gabatar da takardarsa, Jakadan ya bayyana muhimmancin rawar da matasa ke takawa wajen sauya tattalin arziƙi da zamantakewa, yana mai cewa Bangladesh da Nijeriya dukkansu suna da yawan matasa masu kuzari waɗanda suke da babbar damar amfani.

 

Ya kawo misalan ƙirkire-ƙirkiren matasa, haɗin gwiwar duniya da cigaban zamantakewa, yana mai bayyana cewa matasa a sassa daban-daban na duniya suna taka rawar gani wajen kawo canji.

 

Ya kuma ce ɗaliban MAAUN suna cikin sahun gaba wajen wannan tafiya ta duniya, yana yabawa jami’ar saboda ingantaccen yanayin koyarwa, hangen nesa na shugabanci da jajircewar da take da shi wajen ci gaban ɗalibai.

 

A ƙarshe, shugaban ‘School of Postgraduate’ na jami’ar, Farfesa Ibrahim Maigari, ya yaba wa jakadan Bangladesh saboda zaɓar MAAUN a matsayin jami’ar da za ta karɓi irin wannan muhimmin taro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.