ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Bangladesh Ya Yaba Wa MAAUN, Ya Buƙaci A Kafa Reshen Jami’ar A Ƙasarsa 

by Bello Hamza and Sulaiman
6 months ago
MAAUN

Jakadan Bangladesh a Nijeriya, Mista Miah Mainul Kabir, ya yi kira da a kafa reshen Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) a ƙasar Bangladesh.

 

Mista Mainul Kabir ya bayyana wannan buƙata ne a lokacin da ya ziyarci MAAUN Kano a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa buɗe reshen MAAUN a Bangladesh zai ƙara fito da jami’ar a idon duniya wajen haɓaka ilimi da basirar ƙere-ƙere a matakin ƙasa da ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kano Ta Fara Ɗaukar Matakan Daƙile Dawowar Masu Achaba
  • Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (2)

Jakadan ya yaba wa MAAUN bisa yadda shahararta yake ƙaruwa wajen ingancin karatu da bincike kan ƙirkire-ƙirkire, yana mai cewa jajircewar jami’ar wajen ƙirƙira ta zama abin koyi ga sabbin jami’o’i a faɗin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Jakadan ya kasance a jami’ar ne domin gabatar da lacca mai taken: “Amfani da Ƙwarewar Matasa wajen Tattalin Arziki da Cigaban Zamantakewa.”

 

Laccar wadda Ofishin Jakadancin Bangladesh da ke Abuja tare da haɗin gwiwar MAAUN suka shirya, ta yi nufin ƙarfafa matasa domin gina kyakkyawar makoma ga kansu da ƙasa baki ɗaya.

 

Tun kafin fara laccar, hukumar gudanarwar jami’ar da jakadan Bangladesh da tawagarsa sun yi dogon zama kan fannoni daban-daban na yiwuwar haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da ƙasar Bangladesh.

 

Ya jaddada ƙoƙarin da ofishin jakadancin ke yi na tuntuɓar gwamnatoci, cibiyoyi da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin samar da haɗin gwiwar da za ta haifar da ci gaba mai ma’ana.

 

Daga bisani, an zagaya da Jakadan da tawagarsa wasu muhimman sassa na jami’ar, ciki har da MAAUN Innovation Hub da ke cikin School of Computing, inda ya duba kayan aiki da ake amfani da su a wurin.

 

A jawabinsa na maraba, Shugaban MAAUN, Farfesa (Dr.) Mohammad Israr, ya ce wannan lacca daga jakadan Bangladesh shaida ce ta jajircewar MAAUN wajen gina haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da kuma ƙarfafa matasa.

 

Ya jaddada buƙatar samar wa matasa ƙwarewa, ilimi da damar da ake buƙata domin su taka rawar gani wajen kawo cigaba mai ma’ana.

 

A nasa ɓangaren, Mataimakin Shugaban Jami’ar (ɓangaren gudanarwa), Dr. Habib Awaisu Abubakar, ya yaba wa Ofishin Jakadancin Bangladesh da kuma MAAUN bisa yunƙurin faɗaɗa haɗin gwiwa domin ƙarfafa fannin ilimi da ci gaba.

 

A yayin gabatar da takardarsa, Jakadan ya bayyana muhimmancin rawar da matasa ke takawa wajen sauya tattalin arziƙi da zamantakewa, yana mai cewa Bangladesh da Nijeriya dukkansu suna da yawan matasa masu kuzari waɗanda suke da babbar damar amfani.

 

Ya kawo misalan ƙirkire-ƙirkiren matasa, haɗin gwiwar duniya da cigaban zamantakewa, yana mai bayyana cewa matasa a sassa daban-daban na duniya suna taka rawar gani wajen kawo canji.

 

Ya kuma ce ɗaliban MAAUN suna cikin sahun gaba wajen wannan tafiya ta duniya, yana yabawa jami’ar saboda ingantaccen yanayin koyarwa, hangen nesa na shugabanci da jajircewar da take da shi wajen ci gaban ɗalibai.

 

A ƙarshe, shugaban ‘School of Postgraduate’ na jami’ar, Farfesa Ibrahim Maigari, ya yaba wa jakadan Bangladesh saboda zaɓar MAAUN a matsayin jami’ar da za ta karɓi irin wannan muhimmin taro.

MAAUN
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
MAAUN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.