ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Bangladesh Ya Yaba Wa MAAUN, Ya Buƙaci A Kafa Reshen Jami’ar A Ƙasarsa 

by Bello Hamza and Sulaiman
7 months ago
MAAUN

Jakadan Bangladesh a Nijeriya, Mista Miah Mainul Kabir, ya yi kira da a kafa reshen Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN) a ƙasar Bangladesh.

 

Mista Mainul Kabir ya bayyana wannan buƙata ne a lokacin da ya ziyarci MAAUN Kano a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa buɗe reshen MAAUN a Bangladesh zai ƙara fito da jami’ar a idon duniya wajen haɓaka ilimi da basirar ƙere-ƙere a matakin ƙasa da ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Kano Ta Fara Ɗaukar Matakan Daƙile Dawowar Masu Achaba
  • Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (2)

Jakadan ya yaba wa MAAUN bisa yadda shahararta yake ƙaruwa wajen ingancin karatu da bincike kan ƙirkire-ƙirkire, yana mai cewa jajircewar jami’ar wajen ƙirƙira ta zama abin koyi ga sabbin jami’o’i a faɗin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Jakadan ya kasance a jami’ar ne domin gabatar da lacca mai taken: “Amfani da Ƙwarewar Matasa wajen Tattalin Arziki da Cigaban Zamantakewa.”

 

Laccar wadda Ofishin Jakadancin Bangladesh da ke Abuja tare da haɗin gwiwar MAAUN suka shirya, ta yi nufin ƙarfafa matasa domin gina kyakkyawar makoma ga kansu da ƙasa baki ɗaya.

 

Tun kafin fara laccar, hukumar gudanarwar jami’ar da jakadan Bangladesh da tawagarsa sun yi dogon zama kan fannoni daban-daban na yiwuwar haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da ƙasar Bangladesh.

 

Ya jaddada ƙoƙarin da ofishin jakadancin ke yi na tuntuɓar gwamnatoci, cibiyoyi da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin samar da haɗin gwiwar da za ta haifar da ci gaba mai ma’ana.

 

Daga bisani, an zagaya da Jakadan da tawagarsa wasu muhimman sassa na jami’ar, ciki har da MAAUN Innovation Hub da ke cikin School of Computing, inda ya duba kayan aiki da ake amfani da su a wurin.

 

A jawabinsa na maraba, Shugaban MAAUN, Farfesa (Dr.) Mohammad Israr, ya ce wannan lacca daga jakadan Bangladesh shaida ce ta jajircewar MAAUN wajen gina haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da kuma ƙarfafa matasa.

 

Ya jaddada buƙatar samar wa matasa ƙwarewa, ilimi da damar da ake buƙata domin su taka rawar gani wajen kawo cigaba mai ma’ana.

 

A nasa ɓangaren, Mataimakin Shugaban Jami’ar (ɓangaren gudanarwa), Dr. Habib Awaisu Abubakar, ya yaba wa Ofishin Jakadancin Bangladesh da kuma MAAUN bisa yunƙurin faɗaɗa haɗin gwiwa domin ƙarfafa fannin ilimi da ci gaba.

 

A yayin gabatar da takardarsa, Jakadan ya bayyana muhimmancin rawar da matasa ke takawa wajen sauya tattalin arziƙi da zamantakewa, yana mai cewa Bangladesh da Nijeriya dukkansu suna da yawan matasa masu kuzari waɗanda suke da babbar damar amfani.

 

Ya kawo misalan ƙirkire-ƙirkiren matasa, haɗin gwiwar duniya da cigaban zamantakewa, yana mai bayyana cewa matasa a sassa daban-daban na duniya suna taka rawar gani wajen kawo canji.

 

Ya kuma ce ɗaliban MAAUN suna cikin sahun gaba wajen wannan tafiya ta duniya, yana yabawa jami’ar saboda ingantaccen yanayin koyarwa, hangen nesa na shugabanci da jajircewar da take da shi wajen ci gaban ɗalibai.

 

A ƙarshe, shugaban ‘School of Postgraduate’ na jami’ar, Farfesa Ibrahim Maigari, ya yaba wa jakadan Bangladesh saboda zaɓar MAAUN a matsayin jami’ar da za ta karɓi irin wannan muhimmin taro.

MAAUN
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
MAAUN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.