• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Sin Ya Musanta Zargin Danawa Afirka Tarkon Bashi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Sin Ya Musanta Zargin Danawa Afirka Tarkon Bashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jakadan kasar Sin a Amurka Qin Gang, ya karyata zargin cewa wai Sin na danawa kasashen nahiyar Afirka tarkon bashi. Jakadan ya kara da cewa, kamata ya yi nahiyar Afirka ta zama wurin hadin gwiwar kasa da kasa, maimakon wani fage na gwabza takara, domin cimma burikan siyasar yankunan.

Tsokacin jakada Qin Gang, ya zo ne a jajiberin taron yaukaka dangantakar Amurka da kasashen Afirka, wanda shugaba Joe Biden zai jagoranta a birnin Washington.

  • Sin: Afrika Ba Fagen Dagar Takarar Kasashen Yamma Ba Ce

Yayin kwarya-kwaryar tattaunawa da kafar watsa labarai ta Semafor dake Amurka a jiya Talata, gabanin bude taron na Washington, Qin ya ce “Ko kadan jarin da Sin ke zubawa a Afirka, da ma tallafin kudade da kasar ke baiwa nahiyar ba tarkon bashi ba ne”.

Jakadan na Sin ya yi fashin baki, game da sakamakon wani bincike da cibiyar “Debt Justice” dake Birtaniya ta wallafa a watan Yuli, inda ya ce adadin bashin da hukumomin kudi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, ya ninka wanda Sin ke bin kasashen nahiyar har sau 3, kuma yawan kudin ruwa da hukumomin kudin na yammacin duniya ke cazar kasashen Afirka ya ninka na kasar Sin.
Bugu da kari, jakada Qin ya tabo batun dage wa’adin biyan bashi da kasashen G20 suka gabatar, inda ya ce Sin na kan gaba wajen aiwatar da wannan manufa, inda ta zamo ta farko wajen dage wa’adin biyan bashin da take bin kasashe daban daban, cikin daukacin kasashe mambobin kungiyar ta G20.

Game da taron na Amurka da kasashen Afirka, jakadan ya ce yana fatan Amurka za ta fito da kwararan matakai da za su ingiza ci gaba da wadatar nahiyar Afirka. Kaza lika ya yi kira ga Amurka da ta yi hadin gwiwa da Sin, ta yadda a matsayin su na kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, kuma mambobin dindindin a kwamitin tsaron MDD, za su iya hada karfi da karfe wajen bunkasa zaman lafiya, da tsaro da bunkasar nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Har ila yau, ya kamata su sauke nauyin dake wuyansu, kasancewarsu manyan kasashe da ya dace su cika alkawuran da suka dauka a matakin kasa da kasa.

Taron birnin Washington na bunkasa hadin gwiwar Amurka da kasashen Afirka, zai gudana ne tsakanin ranakun Talata zuwa Alhamis, ya kuma hallara shugabanni daga kasashen Afirka 49, da kuma sassa daban daban na masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci da cinikayya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qatar 2022: An Soke Wasu Jiragen Da Za Su Yi Jigilar ‘Yan Morocco Zuwa Qatar

Next Post

Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

Related

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

60 minutes ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

20 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

21 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

22 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

23 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

1 day ago
Next Post
Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.