• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Sin Ya Musanta Zargin Danawa Afirka Tarkon Bashi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Sin Ya Musanta Zargin Danawa Afirka Tarkon Bashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jakadan kasar Sin a Amurka Qin Gang, ya karyata zargin cewa wai Sin na danawa kasashen nahiyar Afirka tarkon bashi. Jakadan ya kara da cewa, kamata ya yi nahiyar Afirka ta zama wurin hadin gwiwar kasa da kasa, maimakon wani fage na gwabza takara, domin cimma burikan siyasar yankunan.

Tsokacin jakada Qin Gang, ya zo ne a jajiberin taron yaukaka dangantakar Amurka da kasashen Afirka, wanda shugaba Joe Biden zai jagoranta a birnin Washington.

  • Sin: Afrika Ba Fagen Dagar Takarar Kasashen Yamma Ba Ce

Yayin kwarya-kwaryar tattaunawa da kafar watsa labarai ta Semafor dake Amurka a jiya Talata, gabanin bude taron na Washington, Qin ya ce “Ko kadan jarin da Sin ke zubawa a Afirka, da ma tallafin kudade da kasar ke baiwa nahiyar ba tarkon bashi ba ne”.

Jakadan na Sin ya yi fashin baki, game da sakamakon wani bincike da cibiyar “Debt Justice” dake Birtaniya ta wallafa a watan Yuli, inda ya ce adadin bashin da hukumomin kudi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, ya ninka wanda Sin ke bin kasashen nahiyar har sau 3, kuma yawan kudin ruwa da hukumomin kudin na yammacin duniya ke cazar kasashen Afirka ya ninka na kasar Sin.
Bugu da kari, jakada Qin ya tabo batun dage wa’adin biyan bashi da kasashen G20 suka gabatar, inda ya ce Sin na kan gaba wajen aiwatar da wannan manufa, inda ta zamo ta farko wajen dage wa’adin biyan bashin da take bin kasashe daban daban, cikin daukacin kasashe mambobin kungiyar ta G20.

Game da taron na Amurka da kasashen Afirka, jakadan ya ce yana fatan Amurka za ta fito da kwararan matakai da za su ingiza ci gaba da wadatar nahiyar Afirka. Kaza lika ya yi kira ga Amurka da ta yi hadin gwiwa da Sin, ta yadda a matsayin su na kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, kuma mambobin dindindin a kwamitin tsaron MDD, za su iya hada karfi da karfe wajen bunkasa zaman lafiya, da tsaro da bunkasar nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Har ila yau, ya kamata su sauke nauyin dake wuyansu, kasancewarsu manyan kasashe da ya dace su cika alkawuran da suka dauka a matakin kasa da kasa.

Taron birnin Washington na bunkasa hadin gwiwar Amurka da kasashen Afirka, zai gudana ne tsakanin ranakun Talata zuwa Alhamis, ya kuma hallara shugabanni daga kasashen Afirka 49, da kuma sassa daban daban na masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci da cinikayya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qatar 2022: An Soke Wasu Jiragen Da Za Su Yi Jigilar ‘Yan Morocco Zuwa Qatar

Next Post

Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

7 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

8 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

10 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

10 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

12 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

12 hours ago
Next Post
Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

LABARAI MASU NASABA

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.