ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Sin Ya Musanta Zargin Danawa Afirka Tarkon Bashi

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Jakadan kasar Sin a Amurka Qin Gang, ya karyata zargin cewa wai Sin na danawa kasashen nahiyar Afirka tarkon bashi. Jakadan ya kara da cewa, kamata ya yi nahiyar Afirka ta zama wurin hadin gwiwar kasa da kasa, maimakon wani fage na gwabza takara, domin cimma burikan siyasar yankunan.

Tsokacin jakada Qin Gang, ya zo ne a jajiberin taron yaukaka dangantakar Amurka da kasashen Afirka, wanda shugaba Joe Biden zai jagoranta a birnin Washington.

  • Sin: Afrika Ba Fagen Dagar Takarar Kasashen Yamma Ba Ce

Yayin kwarya-kwaryar tattaunawa da kafar watsa labarai ta Semafor dake Amurka a jiya Talata, gabanin bude taron na Washington, Qin ya ce “Ko kadan jarin da Sin ke zubawa a Afirka, da ma tallafin kudade da kasar ke baiwa nahiyar ba tarkon bashi ba ne”.

ADVERTISEMENT

Jakadan na Sin ya yi fashin baki, game da sakamakon wani bincike da cibiyar “Debt Justice” dake Birtaniya ta wallafa a watan Yuli, inda ya ce adadin bashin da hukumomin kudi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, ya ninka wanda Sin ke bin kasashen nahiyar har sau 3, kuma yawan kudin ruwa da hukumomin kudin na yammacin duniya ke cazar kasashen Afirka ya ninka na kasar Sin.
Bugu da kari, jakada Qin ya tabo batun dage wa’adin biyan bashi da kasashen G20 suka gabatar, inda ya ce Sin na kan gaba wajen aiwatar da wannan manufa, inda ta zamo ta farko wajen dage wa’adin biyan bashin da take bin kasashe daban daban, cikin daukacin kasashe mambobin kungiyar ta G20.

Game da taron na Amurka da kasashen Afirka, jakadan ya ce yana fatan Amurka za ta fito da kwararan matakai da za su ingiza ci gaba da wadatar nahiyar Afirka. Kaza lika ya yi kira ga Amurka da ta yi hadin gwiwa da Sin, ta yadda a matsayin su na kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, kuma mambobin dindindin a kwamitin tsaron MDD, za su iya hada karfi da karfe wajen bunkasa zaman lafiya, da tsaro da bunkasar nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Har ila yau, ya kamata su sauke nauyin dake wuyansu, kasancewarsu manyan kasashe da ya dace su cika alkawuran da suka dauka a matakin kasa da kasa.

Taron birnin Washington na bunkasa hadin gwiwar Amurka da kasashen Afirka, zai gudana ne tsakanin ranakun Talata zuwa Alhamis, ya kuma hallara shugabanni daga kasashen Afirka 49, da kuma sassa daban daban na masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci da cinikayya. (Saminu Alhassan)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

Da Gaske Ronaldo Ya Fi Messi Samun Lambobin Yabo?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.