• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Kano Na Ƙaunar Alh. Aminu Ado Bayero Saboda Ƙaunarsa Da Zaman Lafiya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan kwanakin nan wasu maganganu na ta yawo da karakaina musanman a shafukan sada zumunta a kan batun da ya shafi Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado Abdullahi Bayero da Masarautar Kanon da ke Arewacin Nijeriya.

LEADERSHIP HAUSA ta bi kadin wannan batun don jin ra’ayoyin jama’a game da Sarkin Kano da cece-kucan da ake kan bukatar da kungiya da ake kira da ‘yan dangwale suka gabatarwa zauren majalisar dokokin Jihar Kano, kan ta rushe sababbin masarautun Kano 4 da batun sake dawo da Sarkin Kano na 14, Sanusi Lamido Sanusi. Kan haka mun bibiyi ra’ayoyin wasu Kanawa kan batun.

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
  • Kungiyar ‘Yan Dangwale Ta Nemi Majalisa Ta Tsige Sarakunan Kano 5 Da Dawo Da Sanusi
  • Za Mu Cigaba Da Fadakarwa Kan Dorewar  Zaman Lafiya Tsakanin Arewa Da Kudu – Sarkin Kano

Wani mai bibiyar al’amuran da suka shafi masarautar Kano da ya bukaci mu boye sunansa, ya bayyana mana cewa, mutanen Kano ba za su taba kaunar a raba su da Sarkin su ba, don suna kaunarsa saboda kaunarsa da son zaman lafiya ga duk Jama’ar Kano da mutanen da ke Fadar Kano, ya ce, misali na farko da zamu iya kallo don gane karamcin Sarkin Kanon tun gabanin ya zama Sarki, yana cewa, ” Mai martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, yana cikin mutane na farko da suka yi wa, Muhammad Sunusi II, mubaya’a da ba shi gudunmowar da babu wanda ya ba shi tun daga sanda ya zama Sarki har zuwa lokacin da aka fadada Masarautun Kano zuwa gida biyar, ”

“A lokacin da aka nada Sarki Muhammad Sunusi II, al’umma sun yi bore na rashin aminta da nadin da aka yi masa, wanda har ta kai aka kwashe kwanaki 3 ana ta gudanar da zanga-zanga da kona tayoyi a birnin Kano, komai ya tsaya cak aka hana shiga gidan Dabo, a karshe gwmanatin wancan lokacin sai da ta yi amfani da ‘yan tauri wajen rako sarkin don shiga gidan Dabo.” Cewarsa.

Ya ci gaba da bayyana cewa; “ A lokacin da Sanusi ya shiga gidan Dabo, wasu daga cikin hakimai da yawa suka ki zuwa yin mubayi’a sai da shi Sarkin na yanzu Alh. Aminu Ado Bayero, ya bi su daya bayan daya yana musu nasiha kan su zo su yi wa l, Sanusi Lamido, mubaya’a tunda Allah ya ba shi, hatta ‘ya’yan marigayi Sarkin Kano Ado Bayero, Sarkin Kano Aminu ne ya hada kan su don su mara wa Sarki Sunusi baya ya ci gaba da gudanar da sha’anin mulkinsa cikin natsuwa.” Cewarsa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

A bangare guda wasu masoya Sarkin na Kano, Alh. Aminu Ado Bayero, na ganin cewa tun asali ma shi ne ya nuna wa Sarki Sanusi hanyoyin da zai bi don samun soyayya daga al’ummar Kano, suka ce ta haka ne ma ya samu gagarumar nasara wajen samun soyayya jama’ar Kano a wancan lokacin.

Bangaren Muhammadu Sanusi ll

Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll
Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll

A bangare guda, su kuwa masu fata da burin dawowar Sarkin Kanon na 14, Malam Muhammadu Sanusi ll, kan karagar masarautar ta Kanon, dalilan su na dawowar tsohon Sarkin Kanon na 14 bai wuce cewa wai an cire Sarkin a wancan lokacin ba bisa ka’ida ba, kuma ba’a bi tanadin doka yayin tube rawanin Sarki Sanusi ll ba.

Wasu na ganin a dawo da Sanusi ll don ya zama an hade masaratun wuri guda da sarki daya rak.

Mai Mazauna Kano ke cewa kan batun?

Wasu mazauna Kanon na cewa indai laifi ne ke saka wa a cire Sarki to babu wanda zai iya fadar ga laifin da Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, ya yi harda za ta kai ga cire shi, kuma duk masu yada maganar a cire shi ba su da wani dalili na laifi ko hujja kan haka, face dai su fake da cewa saboda kawai tsohon Gwamnan Kano Ganduje ne ya nada shi.

Wasu kuwa cewa suke fatan su bai wuce zaman lafiyar Kano ya dore ba, don haka a bar wannan batun na tube rawanin Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado, don gudun kar a hautsina zaman lafiyar Kano, a mayar da hankali wajen yaki da fatara da yunwa da ta addabi jama’a a yanzu.

Mai Gwmanatin Kano ta ce kan batun? 

Har kawo wannan lokacin da muke hada wannan rahoton babu wata magana da ta fito daga bakin gwamnatin jihar kan batun a hukumance. Sai dai ana hango wasu makusanta gwamnatin na aike wa da shagube kan batun masarautun Kanon da ke tayar da kura a yanzu haka a Kano da kafafan sada zumunta na yanar gizo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alhaji Aminu Ado BayerokanoMasarautar KanoMuhammadu Sanusi llSarkin Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Fitar Da Hatsi Ton Dubu 42 Don Rage Tsadar Abinci A Nijeriya

Next Post

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.