• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Kano Na Ƙaunar Alh. Aminu Ado Bayero Saboda Ƙaunarsa Da Zaman Lafiya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan kwanakin nan wasu maganganu na ta yawo da karakaina musanman a shafukan sada zumunta a kan batun da ya shafi Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado Abdullahi Bayero da Masarautar Kanon da ke Arewacin Nijeriya.

LEADERSHIP HAUSA ta bi kadin wannan batun don jin ra’ayoyin jama’a game da Sarkin Kano da cece-kucan da ake kan bukatar da kungiya da ake kira da ‘yan dangwale suka gabatarwa zauren majalisar dokokin Jihar Kano, kan ta rushe sababbin masarautun Kano 4 da batun sake dawo da Sarkin Kano na 14, Sanusi Lamido Sanusi. Kan haka mun bibiyi ra’ayoyin wasu Kanawa kan batun.

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
  • Kungiyar ‘Yan Dangwale Ta Nemi Majalisa Ta Tsige Sarakunan Kano 5 Da Dawo Da Sanusi
  • Za Mu Cigaba Da Fadakarwa Kan Dorewar  Zaman Lafiya Tsakanin Arewa Da Kudu – Sarkin Kano

Wani mai bibiyar al’amuran da suka shafi masarautar Kano da ya bukaci mu boye sunansa, ya bayyana mana cewa, mutanen Kano ba za su taba kaunar a raba su da Sarkin su ba, don suna kaunarsa saboda kaunarsa da son zaman lafiya ga duk Jama’ar Kano da mutanen da ke Fadar Kano, ya ce, misali na farko da zamu iya kallo don gane karamcin Sarkin Kanon tun gabanin ya zama Sarki, yana cewa, ” Mai martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, yana cikin mutane na farko da suka yi wa, Muhammad Sunusi II, mubaya’a da ba shi gudunmowar da babu wanda ya ba shi tun daga sanda ya zama Sarki har zuwa lokacin da aka fadada Masarautun Kano zuwa gida biyar, ”

“A lokacin da aka nada Sarki Muhammad Sunusi II, al’umma sun yi bore na rashin aminta da nadin da aka yi masa, wanda har ta kai aka kwashe kwanaki 3 ana ta gudanar da zanga-zanga da kona tayoyi a birnin Kano, komai ya tsaya cak aka hana shiga gidan Dabo, a karshe gwmanatin wancan lokacin sai da ta yi amfani da ‘yan tauri wajen rako sarkin don shiga gidan Dabo.” Cewarsa.

Ya ci gaba da bayyana cewa; “ A lokacin da Sanusi ya shiga gidan Dabo, wasu daga cikin hakimai da yawa suka ki zuwa yin mubayi’a sai da shi Sarkin na yanzu Alh. Aminu Ado Bayero, ya bi su daya bayan daya yana musu nasiha kan su zo su yi wa l, Sanusi Lamido, mubaya’a tunda Allah ya ba shi, hatta ‘ya’yan marigayi Sarkin Kano Ado Bayero, Sarkin Kano Aminu ne ya hada kan su don su mara wa Sarki Sunusi baya ya ci gaba da gudanar da sha’anin mulkinsa cikin natsuwa.” Cewarsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

A bangare guda wasu masoya Sarkin na Kano, Alh. Aminu Ado Bayero, na ganin cewa tun asali ma shi ne ya nuna wa Sarki Sanusi hanyoyin da zai bi don samun soyayya daga al’ummar Kano, suka ce ta haka ne ma ya samu gagarumar nasara wajen samun soyayya jama’ar Kano a wancan lokacin.

Bangaren Muhammadu Sanusi ll

Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll
Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll

A bangare guda, su kuwa masu fata da burin dawowar Sarkin Kanon na 14, Malam Muhammadu Sanusi ll, kan karagar masarautar ta Kanon, dalilan su na dawowar tsohon Sarkin Kanon na 14 bai wuce cewa wai an cire Sarkin a wancan lokacin ba bisa ka’ida ba, kuma ba’a bi tanadin doka yayin tube rawanin Sarki Sanusi ll ba.

Wasu na ganin a dawo da Sanusi ll don ya zama an hade masaratun wuri guda da sarki daya rak.

Mai Mazauna Kano ke cewa kan batun?

Wasu mazauna Kanon na cewa indai laifi ne ke saka wa a cire Sarki to babu wanda zai iya fadar ga laifin da Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, ya yi harda za ta kai ga cire shi, kuma duk masu yada maganar a cire shi ba su da wani dalili na laifi ko hujja kan haka, face dai su fake da cewa saboda kawai tsohon Gwamnan Kano Ganduje ne ya nada shi.

Wasu kuwa cewa suke fatan su bai wuce zaman lafiyar Kano ya dore ba, don haka a bar wannan batun na tube rawanin Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado, don gudun kar a hautsina zaman lafiyar Kano, a mayar da hankali wajen yaki da fatara da yunwa da ta addabi jama’a a yanzu.

Mai Gwmanatin Kano ta ce kan batun? 

Har kawo wannan lokacin da muke hada wannan rahoton babu wata magana da ta fito daga bakin gwamnatin jihar kan batun a hukumance. Sai dai ana hango wasu makusanta gwamnatin na aike wa da shagube kan batun masarautun Kanon da ke tayar da kura a yanzu haka a Kano da kafafan sada zumunta na yanar gizo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alhaji Aminu Ado BayerokanoMasarautar KanoMuhammadu Sanusi llSarkin Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Fitar Da Hatsi Ton Dubu 42 Don Rage Tsadar Abinci A Nijeriya

Next Post

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

17 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

23 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

1 day ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

1 day ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

2 days ago
Next Post
Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.