ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Kano Na Ƙaunar Alh. Aminu Ado Bayero Saboda Ƙaunarsa Da Zaman Lafiya

by Leadership Hausa
2 years ago
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

A ‘yan kwanakin nan wasu maganganu na ta yawo da karakaina musanman a shafukan sada zumunta a kan batun da ya shafi Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado Abdullahi Bayero da Masarautar Kanon da ke Arewacin Nijeriya.

LEADERSHIP HAUSA ta bi kadin wannan batun don jin ra’ayoyin jama’a game da Sarkin Kano da cece-kucan da ake kan bukatar da kungiya da ake kira da ‘yan dangwale suka gabatarwa zauren majalisar dokokin Jihar Kano, kan ta rushe sababbin masarautun Kano 4 da batun sake dawo da Sarkin Kano na 14, Sanusi Lamido Sanusi. Kan haka mun bibiyi ra’ayoyin wasu Kanawa kan batun.

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero
  • Kungiyar ‘Yan Dangwale Ta Nemi Majalisa Ta Tsige Sarakunan Kano 5 Da Dawo Da Sanusi
  • Za Mu Cigaba Da Fadakarwa Kan Dorewar  Zaman Lafiya Tsakanin Arewa Da Kudu – Sarkin Kano

Wani mai bibiyar al’amuran da suka shafi masarautar Kano da ya bukaci mu boye sunansa, ya bayyana mana cewa, mutanen Kano ba za su taba kaunar a raba su da Sarkin su ba, don suna kaunarsa saboda kaunarsa da son zaman lafiya ga duk Jama’ar Kano da mutanen da ke Fadar Kano, ya ce, misali na farko da zamu iya kallo don gane karamcin Sarkin Kanon tun gabanin ya zama Sarki, yana cewa, ” Mai martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, yana cikin mutane na farko da suka yi wa, Muhammad Sunusi II, mubaya’a da ba shi gudunmowar da babu wanda ya ba shi tun daga sanda ya zama Sarki har zuwa lokacin da aka fadada Masarautun Kano zuwa gida biyar, ”

ADVERTISEMENT

“A lokacin da aka nada Sarki Muhammad Sunusi II, al’umma sun yi bore na rashin aminta da nadin da aka yi masa, wanda har ta kai aka kwashe kwanaki 3 ana ta gudanar da zanga-zanga da kona tayoyi a birnin Kano, komai ya tsaya cak aka hana shiga gidan Dabo, a karshe gwmanatin wancan lokacin sai da ta yi amfani da ‘yan tauri wajen rako sarkin don shiga gidan Dabo.” Cewarsa.

Ya ci gaba da bayyana cewa; “ A lokacin da Sanusi ya shiga gidan Dabo, wasu daga cikin hakimai da yawa suka ki zuwa yin mubayi’a sai da shi Sarkin na yanzu Alh. Aminu Ado Bayero, ya bi su daya bayan daya yana musu nasiha kan su zo su yi wa l, Sanusi Lamido, mubaya’a tunda Allah ya ba shi, hatta ‘ya’yan marigayi Sarkin Kano Ado Bayero, Sarkin Kano Aminu ne ya hada kan su don su mara wa Sarki Sunusi baya ya ci gaba da gudanar da sha’anin mulkinsa cikin natsuwa.” Cewarsa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

A bangare guda wasu masoya Sarkin na Kano, Alh. Aminu Ado Bayero, na ganin cewa tun asali ma shi ne ya nuna wa Sarki Sanusi hanyoyin da zai bi don samun soyayya daga al’ummar Kano, suka ce ta haka ne ma ya samu gagarumar nasara wajen samun soyayya jama’ar Kano a wancan lokacin.

Bangaren Muhammadu Sanusi ll

Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll
Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll

A bangare guda, su kuwa masu fata da burin dawowar Sarkin Kanon na 14, Malam Muhammadu Sanusi ll, kan karagar masarautar ta Kanon, dalilan su na dawowar tsohon Sarkin Kanon na 14 bai wuce cewa wai an cire Sarkin a wancan lokacin ba bisa ka’ida ba, kuma ba’a bi tanadin doka yayin tube rawanin Sarki Sanusi ll ba.

Wasu na ganin a dawo da Sanusi ll don ya zama an hade masaratun wuri guda da sarki daya rak.

Mai Mazauna Kano ke cewa kan batun?

Wasu mazauna Kanon na cewa indai laifi ne ke saka wa a cire Sarki to babu wanda zai iya fadar ga laifin da Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero, ya yi harda za ta kai ga cire shi, kuma duk masu yada maganar a cire shi ba su da wani dalili na laifi ko hujja kan haka, face dai su fake da cewa saboda kawai tsohon Gwamnan Kano Ganduje ne ya nada shi.

Wasu kuwa cewa suke fatan su bai wuce zaman lafiyar Kano ya dore ba, don haka a bar wannan batun na tube rawanin Sarkin Kano, Alh. Aminu Ado, don gudun kar a hautsina zaman lafiyar Kano, a mayar da hankali wajen yaki da fatara da yunwa da ta addabi jama’a a yanzu.

Mai Gwmanatin Kano ta ce kan batun? 

Har kawo wannan lokacin da muke hada wannan rahoton babu wata magana da ta fito daga bakin gwamnatin jihar kan batun a hukumance. Sai dai ana hango wasu makusanta gwamnatin na aike wa da shagube kan batun masarautun Kanon da ke tayar da kura a yanzu haka a Kano da kafafan sada zumunta na yanar gizo.

Kano
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.