ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yan Nijeriya Na Fama Da Jabun Kayan Masarufi Baya Ga Tsadar Rayuwa

by Bello Hamza and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Jabun kaya

‘Yan Nijeriya da dama na ci gaba da nuna damuwarsu kan yawaitar jabun magunguna da abubuwan sha da kayan abinci da sauran kayayyaki a kasar.

Kan haka ne Suka bukaci hukumomin da abin ya shafa su fara gudanar da wani cikakken bincike na kasa kan lamarin da kuma hanzarta sauya yanayin don kauce wa tabarbarewar yanayin kiwon lafiya da sauran abubuwan da ke faruwa.

  • Za Mu Ci Gaba Da Aiwatar Da Abubuwan Da Suka Sa LEADERSHIP Ta Karrama Mu – Gerawa
  • Xi Ya Taya Nangolo Mbumba Murnar Zama Shugaban Kasar Namibiya

Sakamakon binciken ma’aikatar hako ma’adanai da LEADERSHIP ta gano ya nuna cewa magunguna marasa inganci ne ke haddasa mutuwar mutane 500,000 duk shekara a yankin Kudu da hamadar Sahara.

ADVERTISEMENT

Rahoton ya kuma nuna cewa, kusan mutum 267,000 ne ke mutuwa a duk shekara sakamakon amfani da jabun magungunan zazzabin cizon sauro da marasa inganci.

Mutane da dama sun shiga shafukan intanet don yin kira ga Hukumar Kula Da Ingancin Abinci Da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) da ta gudanar da bincike tare da fitar da ingantattun matakan da za a bi don magance yawaitar jabun kayayyakin a kasuwannin NIjeriya.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Wani dan kasuwa a sananniyar kasuwar Utako da ke Abuja, Ugochukwu Henry, ya ce rahoton ya shafi harkokin kasuwanci, amma hakan bai hana mutane sayen kayayyaki a kasuwar ba.

Wata kwastoma a kasuwar, Ruth Ode, ta ce halin da ake ciki matsin tattalin arzikin kasar ne ke haddasa wannan barazana.

Wani kwararre a fannin lafiya ya ce akwai bukatar a kara kwantar da hankulan mutanen da abin ya shafa domin hakan na iya haifar da annoba.

Kwararru sun shaida wa LEADERSHIP cewa yawaitar jabun kayayyaki da marasa inganci a kasuwannin Nijeriya da dama, tare da amfani da su na haifar da karuwar mace-mace a kasar.

Suka ce yawaitar magungunan jabu cin zarafi ne ga masana’antar kiwon lafiya ta kasar, inda suka bayyana cewa hakan na haifar da asarar rayuka da kuma raunana kwarin gwiwa kan magunguna, da ma’aikatan kiwon lafiya, da ma daukacin tsarin kiwon lafiya.

 

Mafi yawan jabun kayayyakin abinci a Nijeriya

Bincike ya nuna cewa kayan abinci na jabu da aka fi yawaita yi a Nijeriya sun hada da jabun magunguna, shinkafa jabu, gurbataccen man kayan lambu, jabun barasa da kayan abinci da kwanankin watan amfani da su suka kare da kuma marasa inganci.

Wadannan samfuran ba koyaushe suke cika ka’idojin aminci da inganci ba, suna haifar da hadari ga masu amfani da su.

A watan da ya gabata ne Hukumar Kula da Ingancin Abinci Da Magunguna Ta Kasa (NAFDAC) ta gano wasu jabun kayayyaki a kasuwar Ezukwu (Cemetery Market) dake garin Aba, Jihar Abia.

Hakan ya jawo martani daga masu ruwa da tsaki a fannin kiwon lafiya.

Shiga tsakanin da hukumar NAFDAC ta yi ya kai ga kwace kusan kayayyakin da kwanakin watansu ya kare 2000, da suka hada da barasa, abubuwan sha, da sauran abubuwan da suka kare. Wannan matakin ya yi sanadin rufe shaguna sama da 240 da ke aiki a matsayin masana’antu, da kera kayayyaki, da sake gyarawa, da kuma sayar da kayayyakin jabu cikin rashin tsafta, a cewar sanarwar da hukumar abinci ta fitar.

 

Tasirin jabun abinci ga tattalin arziki

Bayan hadarin lafiya, samfuran kayan jabu suna kuma haifar da illa ga tattalin arziki.

Wani kiyasi na PricewaterhouseCoopers (PwC) ya nuna cewa Nijeriya na yin asarar kusan Naira biliyan 200 a duk shekara saboda jabun magunguna, ban da magunguna marasa inganci.

A cewar wata kungiya mai zaman kanta, HealthWise International, kididdige madaidaicin tasirin tattalin arziki yana da kalubale; samarwa da rarraba kayan abinci na jabu na iya samun illa mai yawa a duka matakan tattalin arziki wato ‘macroeconomic’ da wadanda suka hada da: kashe kudi akan kiwon lafiya, raguwar yawan aiki, lalata amincin mabukaci, rage yawan amfanin gona, karkatar da albarkatu, hauhawar farashin, tasiri akan kananan sana’o’i, da bambancin zamantakewa da tattalin arziki da sauransu.

 

Dabarun yakar barazanar dake tunkarowa

Masana sun bukaci gwamnati da ta karfafa tsarin mulki, kara dubawa da sa ido, hada kai da masu ruwa da tsaki a masana’antu; kaddamar da yakin wayar da kan jama’a don ilmantar da masu amfani da irin wadannan kayayyaki game da hadarin da ke tattare da abincin jabu da kuma yadda za a gane su; ingantawa da kuma ganowa.

 

Bayar da horo kan don gane nau’in jabun kayan abinci

Pharmacare, wata kungiya ce mai fafutuka kan tabbatar da magungunan gaskiya, ta jero wasu shawarwari da za su taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen gano abubuwa na abincin jabu.

Bincika alamomi da mazubi. Gano kurakuran harufan da aka rubuta sunan magani ko abinci, haruffan da ba a saba gani a jikin kayan ba, ko rashin ingancin rubutu akan murfi. Bincika mazubi da duba alamun tambari, Tabbatar da dacewar bayanin mazubi shin ya ya dace da samfurin ciki, da sauransu

1. Gano lokacin da kwanan watan amfani da kaya zai kare

2. Ku yi amfani da hankalinku wajen gano kamshi, dandano, da kamannin kaya. Idan kamshi ko dandano na samfurin abinci ya saba da irin wanda kuke ci, to zai fi kyau a guje shi. ku yi hankali da sinadari mai tsananin karfi ko kamshi, kawai ya kamata ka sayi kaya daga mashahuran dillalai.

 

A Bude Rumbunan Abinci —Majalisa

Majalisar Wakilai ta nemi gwamnatin tarayya ta dauki matakan ganin an kawo kareshen tsadar abincin da ake fuskanta a sassan kasar nan, ‘yan majalisar sun bayyana haka ne a ganawarsu da ministan kudi Wale Edu da ministan Kaszafin kudi Atiku Abnubakar da kuma ganmna babban bankin Nijeriya Olayemi Carsosor, inda suka nemi bayanai a kan tabarbarewar tattalin arzikin kasa da kuma tsafdar rayuwa da al’ummar Nijeriya kem fuskanta.

A kan haka suka nbukaci wgamnati ta fito abinci da aka adana don kota kwana na sassan kasar nan don a sayar wa al’umma a farashi mai rahusa.

 

Za mu shawo kan lamarin – Gwamnati

A nasa martanin ta gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, tana daukar dukkan matakan da suka kamata na ganin an shawo kan matsalar tsafdar abinci da ta addabi al’umma, kwamiti na musamman na shugaban kasa a kan mastalar abinci ya bayyana cewa, an fara daukar matakan ganin karshen mastalar, cikin matakan sun hada da fitar da abincin da aka ajiye, za a fitar don a sayar wa al’umma a cikin farashi mai rahusa, Miniatan yada kanbarai, Mohammed Idris ya sanar da haka. Ya kuma ce, wgamnati ta damu da zanga zangar tsadar rayuwa da aka yi a wasu sassan Nijeriya.

 

Cin Hanci Da Rashawa Ne Silar Matsalar – Dattawan Arewa

Ita kuwa kungiyar dattawan arewa ta nuna damuwarta ne a kan hauhawar farashin kayan abinci a Nijeriya, ta ce in har ba a dauki matakin da ya kamata ba zai iya haifar wa da al’umma babbar matsalar rayuwa.

Jami’in watsa labarai na kungiyar, Abdul-Azeez Suleiman ya sanar da haka, ya ce, dole a dauki jin dadin al’umma da muhimmanci in ana so a zauna lafiya. Ya kuma ce dole gwamnati ta dauki matakin yaki da cin hanci da rashawa wanda sune silar dukkan matsalar da ake fuskanta.

Jabun kaya
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
Jabun kaya
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

Yadda Tsadar Kayan Masarufi Ke Barazanar Raba Auratayya Da Hana Wasu Yin Aure

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.