• English
  • Business News
Sunday, May 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

by Khalid Idris Doya
1 day ago
in Ilimi
0
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da shirya jarabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta kaddamar da wani bita cikin gaggawa kan tsarin Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (UTME) na shekarar 2025, biyo bayan korafe-korafe da dalibai da iyaye ke yi a fadin kasar na tare da zargin rashin bin ka’ida da kuma sabani a sakamakon jarabawar.

Matakin na zuwa ne kwanaki kalilan da hukumar ta sake sakamakon jarabawar bana, inda hukumar ta tabbatar da cewa ta samu jerin korafe-korafe da daman gaske. Dubban dalibai ne dai suka yi fatali da kin amincewa da sakamakon da suka samu a jarabawar, lamarin da ke janyo kokonto da shakku kan ingancin tsarin da ake bi.

  • JAMB Ta Dakatar Da Wasu Jami’anta Saboda Tilastawa Wata Daliba Cire Hijabi
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Dalibai da dama sun shiga shafukan sada zumunta, suna zargin hukumar JAMB da gazawa ta bangaren samun tangardar na’ura da suka yi imanin cewa ya yi illa ga kwazonsu da kokarinsu a yayin jarabawar.

Da yake magana a Abuja, mai magana da yawun hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin ya tabbatar da cewa hukumar tana duba na’urorinta a kai a kai gabanin ma gudanar da jarabawar.

“Muna hanzarta sake duba jarabawarmu na yau da kullun, wanda zai bincika kowane bangare na tsarin UTME, tun daga rajista zuwa jarrabawa da fitar da sakamako,” in ji Benjamin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Ya yi nuni da cewa hukumar tana aiki ne tare da hadin gwiwar abokan huldar waje, da suka hada da kungiyar kwararrun na’urar kwamfuta ta Nijeriya, da manyan masu jarrabawa daga manyan makarantu, da kungiyar ilimi da cibiyar bincike a Afirka. Wadannan hadin gwiwar, in ji shi, suna da nufin samar da ingantaccen bincike da kuma sahihin bincike.

“Idan an gano cewa an samu tangarda a na’ura, to za a dauki matakan gyarawa ba tare da bata wani lokaci ba,” Benjamin ya tabbatar.

Duk da wannan tabbacin da aka bayar, sama da dalibai 8,000 ne suka shigar da korafinsu a hukumance suna cewa an samu matsaloli na na’ura sosai a yayin jarabawa. Abubuwan da aka ruwaito sun hada da daskararrun allon kwamfuta, jinkirin shiga cikin tsarin zana jarabawar daga ita kwanfutar, da karewar zaman jarrabawa ba zato ba tsammani.

Binciken farko na sakamakon UTME na 2025 ya nuna cewa sama da kashi 78 na sama da dalibai miliyan 1.9 sun samu maki kasa da 200 cikin matsakaicin maki 400. Alkaluman sun kara zurfafa shakku na gazawar fasaha ko na tsari.

Benjamin ya ce duk da haka, lamarin ya tsaya kan sakamakon kamar yadda aka fitar a halin yanzu, yana mai bayyana cewa sun yi daidai da hakikanin kwazon da dalibai suka nuna. Har ila yau, ya amince da alhakin hukumar ta binciki duk rahotannin da suka dace na abubuwan da suka faru.

Sai dai hukumar ta nemi a kwantar da hankali har zuwa lokacin da za ta kammala binciko shin an samu matsala a tsarin jarabawar ko kuma gazawar kwazon ɗalibai ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiJambaMakarantaSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Related

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
Ilimi

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

9 hours ago
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)
Ilimi

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

2 days ago
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu
Ilimi

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

3 days ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

3 weeks ago
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Ilimi

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

3 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.