ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
Hero bay

Yankin Hero Bay, ya kasance a cikin kasar China wanda kuma wani yanki ne, ya yakiwasu al’adun kasar.

 

Yankin wanda ke a kauyen Yingdiongwan a birnin Tongguanyi, ya kuma kasance a cikin gundumar Jiulongpo.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

Kazalika, ya kasance mai dauke da abubuwa da dama da kuma ci gaba na zamani.

 

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

kauyuka a China, ana nufin yankunan da suka bunkasa, wadanda suka kasance, sun yi kamance-ceniya da sun anguwanin GRA a Nijeriya da kuma a nahiyar Afirka.

 

A yankin na Hero Bay, an tanadar da tituna inganciyyar wutar lantarki, tsaftatattacen ruwan sha da kuma kafar Inernet

 

Akwai manyan bene masu tsawo a yankin, wadanda tsawonsu ya dara na bene mai hawa biyar, inda kuma aka tanadar wa da yankin, ababen more rayuwa.

 

kananan hukumomi ne, suka gina wadannan matsugunnan, musamman donin a dakile barazanar kwararowa alumma daga kauye, zuwa cikin birane.

 

A gwajin da aka yi na yankunan da su habaka sosai a China, ana buga misali da Hero Bay kan yadda gwamnati ke bai wa alumma kwarin guiwa na su ci gaba da zama a yankunan da suke, musamman ta hayar samar masu tallafin kudi da gidaje.

 

Wannan dabarun, baya ga kara bunkasa fannin aikin noma a kauyukan, sun kuma kara habaka fannin fasaha kimiyya a kauyukan da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

 

Wani mai gudanar da aikin bincike a cibiyar yin bincike a fannin fasaha ta kasar Wang Yongzhong, ya alakanta kauyukan a matsayin guraren da suka yi fice a duniya, da makuntan kasar, suka samar masu da ababen more rayuwa.

 

Samar da hanyoyi na daga cikin ayyukan da gwamnatin China, ke bai wa mahimmanci, musamman domin a samar da damar gudanar da zirga-zirgar gudanar da ayyukan yau da kullum, a cikin sauki.

 

Samar da yankin na Hero Bay, na daga cikin babban misalin mayar da kan gwamnatin kasar, na dakile kwararowar mazauna a karkara, musamman a tsakanin matasa zuwa cikin birane.

 

Wasu biranen sun kasance cike suke da manyan rukunonin gidage, amma wannan sabanin haka ne, a Hero Bay, duba da yadda aka samar da gidaje, ga ‘yan kauyen da ke da ra’ayin zama a cikinsu, wanda kuma za su iya habaka kasuwancinsu da gudanar da aikin noma, tare da kuma samar da makarantu, Asibiti da jami’an tsaro da sauransu.

 

Daura da Hero Bay, akwai masana’antar kera motoci, wadda kuma ke samar da ayyukan yi ga mazauna yankin, ta hanyar goyon bayan ayyuakn shirye-shirye na kananan hukumomi.

 

A cewar Mataimakin Daraktan shirin bayar da horo China, Mista Wu Hao, gwamnatin kasar ta samar da wadannan ababen more rayuwar ne, domin a dakile kwararar mazauna kauyukan zuwa cikin biranen kasar.

 

daya daga cikin mazauna yankin Madam Yang Baozhen, ta tabbatar da wannan maganar ta Mista Wu Hao, inda ta ce, ana karfafawa, musamman matasa guiwa domin su shiga a dama da su, a fannin hada-hadar kasuwancin yankin, wanda hakan ka samar da kauyukan kudaden shiga.

 

Kazalika, mazauna kauyukan da ba su da bukatar shiga fannin noma ko yin aiki a masana’anta, su kan bude gidajen sayar da abinci ko kuma yin wasu kanannan sana’oi.

 

A kauykan, ana kuma bayar da ilimin zamani kyauta, tun daga matakin Firamare zuwa na Sakandare.

 

Bisa tsarin mallakar filaye a kauyukan ba za ka sayi fili ko kuma ka sayar da shi ba, amma za ka iya bayar da jinginarsa, har zuwa tsawon shekaru 50 zuwa 70, wanda daga baya, za ka sabunta jinginar.

 

A cewar wani mai zagaya wa masu yawon bude ido, “A kasar duk wani fili da ke kasar, mallakar gwamnatin kasar ne, wadda kuma kowanne fili, an tsara abinda za a yi a kansa,”

 

A yayin da ake ci gaba da tattauna wa kan batun bunkasa nahiyar Afrika ciki har da Nijeriya, akwai bukatar a rungumi irin wannan tsarin na China, duba da cewa, abu ne, da kwalliya za ta biya kudin Sabulu.

 

Kazalika, ta hanyarin yin hadaka da tsarin samar da hanyoyi na BRI na China hakan zai samar da wata ingantacciyar hadaka ga kasashe masu tasowa da kuma ga cibiyar bunkasa kasuwanci ta kasa da kasa ta AIBO da ke a karkashin ikon ma’aikatar bunkasa kasuwanci ta China, musamman wajen bayar da horo kan dabarun zamani na bunkasa kasuwanci.

 

Hakazalika, ta hanyar rungumar wannan tsarin China, Afirka za ta iya magance yawan kwararowar mazauna karkara, zuwa cikin birane, wanda hakan zai kuma taimaka wa kasashen da ke a Afrika, wajen kara bunkasa tattalin arzikinsu da samar wa da ‘yan Afrika, alkibla mai dorewa.

 

 

Hero bay
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Hero bay
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Hero bay
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Hero bay
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Hero bay
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Next Post
Ta’addanci

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.