Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta bayyana ranar Asabar 28 ga Yuni wadanda basu samu damar rubuta jarabawar shigaa manyan makaranta kamar yadda aka gudanar da ita a fadin tarayyar Nijeriya, cewa za’a gudanar da jarabawar.
Kamar yadda yadda mai ba Hukumar shawara kan harkokin sadarwa,Dakta Fabian Benjamin, ya bayyana ranar Lahadi,jarabawar da wadanda basu samu damar rubuta jarabawar ba lokacin da aka yi, saboda wasu dalilai, dalibai 5,096 ne ba’a samu damar tantance su ba lokacin da aka gudanar da jarabawar.
- Gwamnatin Kano Ta Amince da Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba
- Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Fabian yace wannan lamarin ya shafi jarabawar da aka yi wannan shekarar inda was dalibai 91,742 da sauran wasu basu samu damar rubuta jarabawar ba, ko da ita ainihin jarabawar,ko kuma wadda aka sake bada lokacin domin sauarn wadanda basu samu ba, su samu lokacin da za su sake rubutawa.
An ware dalibai 96,838 wadanda za su sake rubuta jarabawar a cibiyoyi 183 wadanda za a rubuta jarabawa a fadin kasar Nijeriya.Akwai ma wasu da zasu jira tkuna har sai lokacin da aka kammala yin bincike dangane da irin halin da suke ciki .
Ya kara jaddada cewa“Ita jarabawar da za’ayi zata iya biyan bukatun wadanda basu samu damar rubuta jarabawar ba wato 5,096,da kuma wadanda ba’a samu damar cancansu ba,lokacin da aka yi jarabawar.Hakanan ma saboda dama ta,musamman,da aka ba wadanda basu samu damar rubuta jarabawar ba wadda aka yi watannin da suka gabata, dalibai 91,742 wadanda basu samu damar rubuta jarbawar ba,da kuma wadda aka sake rubutawa,za‘a basu dama,amma kwai ta wannan shekarar 2025 UTME.
“Wannan ya nuna dalibai, 96,838 zasu rubuta jarabawa a fadin Nijeriya gaba daya duk ta wannan shekarar ce, 2025,a cibiyoyin rubuta jarabawa,183,yayin da wasu kuma za su jira.”
Hakanan ma Hukumar tace tana nan tana bankado cibiyoyin rubuta jarabawa da ake yin cuwa- cuwa, da kuma wadanda basu cancanta, ace n arubuta jarabawar a wuraren ba, saboda rashin ingancin abubuwan da ake amfani da su lokacin jarabawar.
Akwai wuraren/ cibiyoyin rubuta jarabawa wadanda aka tantance hakan kuwa ya biyo baya binciken kwakwaf da aka yi lokacin da aka yi jarabawar ta gwaji, jarabawar ta sosai,da wadda aka sake rubutawa.Kamar yadda aka bayyana, kuma kamar yadda sakamakon bincike-binciken da aka yi, akwai cibiyoyin rubuta jarabawa,113 wadanda yanzu an dakatar da amfani dasu,ko ba za ‘a,taba tunanin yin amfani da su ba,a dukkan wadansu ayyuka na hukumar ta JAMB.
Daga karshe Fabian ya kara yin bayani dangane da su cibiyoyin rubuta jarabawar an same su da aikata laifin magudin jarabawa daban daban ko su kasance suna da hannu kai tsaye wajen aikata laifukan da basu dace ba lokacin jarabawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp