• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Warware Dambarwar Kayyade Shekarun Shiga Jami’oi

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
JAMB Ta Warware Dambarwar Kayyade Shekarun Shiga Jami’oi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shirya jarabawa manyan makarantu ta kasa (JAMB) ta fasa kwai a kan abinda ta kira “yadda ake jabun lamarin da ya shafi canza shekarun haihuwa ”a kan nambar takardar dan kasa da aka sani NIN wadda ake turawa hukumar domin a canza shekarun da aka sa.

Hukumar irin wannan halin yana da hadari, cutarwa abinda kuma ba dole bane, inda take cewa sai mai bukatar ya samu gurbin karatu ya kai a kalla shekara 16, a lokacin zai cancanci a dauke shi.

  • Kamfani Ya Maka Bankin Globus A Kotu A Kan Karya Yarjejeniyar Bashi
  • GORON JUMA’A

Jami’in hulda da jama’a na hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin, shi ne ya bayyana hakan wajen taron manema labarai ranar Lahadi ta makon da ya gabata a Abuja inda ya ce “Sai wadanda basu kai shekara 16 ba, ba za su samu damar a basu gurbin karatu ba, idan aka yi la’akari da matakin da aka dauka a taron tsarin hukumar na shekarar 2024.”

Duk da yake dai hukumar ta ba dukkan makarantu wa’adin wata daya domin su bayyana duk damar karatun da suka bada wadda ta wuce ka’idarta ta ta tsarin bada guraben karatu wato (CAPS) kafin shekara 2017.

Ya ce “Hukumar ta lura da yadda wasu makarantu suke bada damar guraben karatu ba tare da bin ka’idar ta ba, inda maimakon haka sai suka bi ta gurguwar hanyar su domin aikata abinda bai dace ba.”

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

“Saboda kawo karshen lamarin ya sa hukumar ta yanke shawarar jan layi saboda a daina aikata laifin da bai dace ba, inda ya kara jan hankali inda ya ce dukkan daliban da aka basu gurbin karatu kafin shekarar 2017.Wadanda bayanansu ke tare da shi wa’adin wata daya daga ranar 1 ga Augusta zuwa 31,2024; duk wani gurbin da aka bayar kafin 2017 ba za a amince da shi ba, idan har ba a bayyana hakan ba cikin wata dayan.”

Ya ce an ja kunnen makarantu su yi amfani da umarnin da aka basu, domin kuwa ba za a kara wani wa’adi ba, ba za a sake amincewa da wasu ‘yan makarantar da ba a shigar da bayanansu ba, wadanda ko ma rajista ba su yi da hukumar ba, ba ma a maganar sun rubuta jarabawarta ba’’.

‘’Wannan matakin an dauke shi ne domin ayi maganin yadda ake bada guraben ilimi ba tare da bin ka’ida ba da kuma sa bayanan karya, yayin da da za a rika tabbatar da ana bin dokar CAPS.”

Hakanan hukumar ta nuna rashin jin dadin ta akan abinda ake kira da suna yadda ake bada damar gurbin karatu wato wanda ake yi ko wace rana da wadansu makarantun fasaha da wasu ke yi da hadin bakin wasu Jami’o’i.

Benjamin ya ce “yana da kyau mutane su gane su wadancan nau’oin karatun hukumomin kula da ilimin fasaha da Jami’oi, basu amince da su ba.Dukkansu shigar kutse suke neman su yi ma tsarin ilimin Nijeriya.”

” Wata damfara ce da ake mantawa da masu nagarta kamar yadda tsarin dokar bada guraben karatu ta tanada ga wadanda za su kasance masu zama makaranta,a bi hanyar da bata dace ba wajen amfani da abubuwan da ba kan ka’ida suke ba, domin a samu kudaden da kan ka’ida suke ba. Ta haka sai a bata ma wadanda suke son shiga ta sahiyar hanya, tare da wadanda suke fandararru.

Daliban da basu yi kokarin azo a gani ba ko makin da bai taka kara ya karya ba, lokacin da suka yi jarabawar shiga manyan makarantu, irinsu ne ake jan hankalinsu, su je su yi irin karatun da ko sun kammala zai iya zame masu alakakai.

Ya ce an gano wasu makarantu da suke daukar dalibai da yawa ta hanyar tasarin karatun da ba a amince da shi ba, inda daga karshe su kan hada su tare da wadanda suka zauna a makarantar suke, amma sai su yaye su tare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiDambaruwaJamb
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muhimmancin Bincike A Harkar Ilimi

Next Post

Jami’in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

Related

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

52 minutes ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 hour ago
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
Manyan Labarai

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

6 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu
Manyan Labarai

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

7 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina
Labarai

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

8 hours ago
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su
Labarai

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

10 hours ago
Next Post
Jami’in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

Jami'in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

September 3, 2025
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

September 3, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

September 3, 2025
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

September 3, 2025
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

September 3, 2025
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

September 3, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

September 3, 2025
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

September 3, 2025
Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

September 3, 2025
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.