ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Warware Dambarwar Kayyade Shekarun Shiga Jami’oi

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Jamb

Hukumar shirya jarabawa manyan makarantu ta kasa (JAMB) ta fasa kwai a kan abinda ta kira “yadda ake jabun lamarin da ya shafi canza shekarun haihuwa ”a kan nambar takardar dan kasa da aka sani NIN wadda ake turawa hukumar domin a canza shekarun da aka sa.

Hukumar irin wannan halin yana da hadari, cutarwa abinda kuma ba dole bane, inda take cewa sai mai bukatar ya samu gurbin karatu ya kai a kalla shekara 16, a lokacin zai cancanci a dauke shi.

  • Kamfani Ya Maka Bankin Globus A Kotu A Kan Karya Yarjejeniyar Bashi
  • GORON JUMA’A

Jami’in hulda da jama’a na hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin, shi ne ya bayyana hakan wajen taron manema labarai ranar Lahadi ta makon da ya gabata a Abuja inda ya ce “Sai wadanda basu kai shekara 16 ba, ba za su samu damar a basu gurbin karatu ba, idan aka yi la’akari da matakin da aka dauka a taron tsarin hukumar na shekarar 2024.”

ADVERTISEMENT

Duk da yake dai hukumar ta ba dukkan makarantu wa’adin wata daya domin su bayyana duk damar karatun da suka bada wadda ta wuce ka’idarta ta ta tsarin bada guraben karatu wato (CAPS) kafin shekara 2017.

Ya ce “Hukumar ta lura da yadda wasu makarantu suke bada damar guraben karatu ba tare da bin ka’idar ta ba, inda maimakon haka sai suka bi ta gurguwar hanyar su domin aikata abinda bai dace ba.”

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

“Saboda kawo karshen lamarin ya sa hukumar ta yanke shawarar jan layi saboda a daina aikata laifin da bai dace ba, inda ya kara jan hankali inda ya ce dukkan daliban da aka basu gurbin karatu kafin shekarar 2017.Wadanda bayanansu ke tare da shi wa’adin wata daya daga ranar 1 ga Augusta zuwa 31,2024; duk wani gurbin da aka bayar kafin 2017 ba za a amince da shi ba, idan har ba a bayyana hakan ba cikin wata dayan.”

Ya ce an ja kunnen makarantu su yi amfani da umarnin da aka basu, domin kuwa ba za a kara wani wa’adi ba, ba za a sake amincewa da wasu ‘yan makarantar da ba a shigar da bayanansu ba, wadanda ko ma rajista ba su yi da hukumar ba, ba ma a maganar sun rubuta jarabawarta ba’’.

‘’Wannan matakin an dauke shi ne domin ayi maganin yadda ake bada guraben ilimi ba tare da bin ka’ida ba da kuma sa bayanan karya, yayin da da za a rika tabbatar da ana bin dokar CAPS.”

Hakanan hukumar ta nuna rashin jin dadin ta akan abinda ake kira da suna yadda ake bada damar gurbin karatu wato wanda ake yi ko wace rana da wadansu makarantun fasaha da wasu ke yi da hadin bakin wasu Jami’o’i.

Benjamin ya ce “yana da kyau mutane su gane su wadancan nau’oin karatun hukumomin kula da ilimin fasaha da Jami’oi, basu amince da su ba.Dukkansu shigar kutse suke neman su yi ma tsarin ilimin Nijeriya.”

” Wata damfara ce da ake mantawa da masu nagarta kamar yadda tsarin dokar bada guraben karatu ta tanada ga wadanda za su kasance masu zama makaranta,a bi hanyar da bata dace ba wajen amfani da abubuwan da ba kan ka’ida suke ba, domin a samu kudaden da kan ka’ida suke ba. Ta haka sai a bata ma wadanda suke son shiga ta sahiyar hanya, tare da wadanda suke fandararru.

Daliban da basu yi kokarin azo a gani ba ko makin da bai taka kara ya karya ba, lokacin da suka yi jarabawar shiga manyan makarantu, irinsu ne ake jan hankalinsu, su je su yi irin karatun da ko sun kammala zai iya zame masu alakakai.

Ya ce an gano wasu makarantu da suke daukar dalibai da yawa ta hanyar tasarin karatun da ba a amince da shi ba, inda daga karshe su kan hada su tare da wadanda suka zauna a makarantar suke, amma sai su yaye su tare.

Jamb
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Rahotonni

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
Labarai

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Next Post
Jami’in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

Jami'in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.