ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JAMB Ta Warware Dambarwar Kayyade Shekarun Shiga Jami’oi

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Jamb

Hukumar shirya jarabawa manyan makarantu ta kasa (JAMB) ta fasa kwai a kan abinda ta kira “yadda ake jabun lamarin da ya shafi canza shekarun haihuwa ”a kan nambar takardar dan kasa da aka sani NIN wadda ake turawa hukumar domin a canza shekarun da aka sa.

Hukumar irin wannan halin yana da hadari, cutarwa abinda kuma ba dole bane, inda take cewa sai mai bukatar ya samu gurbin karatu ya kai a kalla shekara 16, a lokacin zai cancanci a dauke shi.

  • Kamfani Ya Maka Bankin Globus A Kotu A Kan Karya Yarjejeniyar Bashi
  • GORON JUMA’A

Jami’in hulda da jama’a na hukumar JAMB, Dakta Fabian Benjamin, shi ne ya bayyana hakan wajen taron manema labarai ranar Lahadi ta makon da ya gabata a Abuja inda ya ce “Sai wadanda basu kai shekara 16 ba, ba za su samu damar a basu gurbin karatu ba, idan aka yi la’akari da matakin da aka dauka a taron tsarin hukumar na shekarar 2024.”

ADVERTISEMENT

Duk da yake dai hukumar ta ba dukkan makarantu wa’adin wata daya domin su bayyana duk damar karatun da suka bada wadda ta wuce ka’idarta ta ta tsarin bada guraben karatu wato (CAPS) kafin shekara 2017.

Ya ce “Hukumar ta lura da yadda wasu makarantu suke bada damar guraben karatu ba tare da bin ka’idar ta ba, inda maimakon haka sai suka bi ta gurguwar hanyar su domin aikata abinda bai dace ba.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

“Saboda kawo karshen lamarin ya sa hukumar ta yanke shawarar jan layi saboda a daina aikata laifin da bai dace ba, inda ya kara jan hankali inda ya ce dukkan daliban da aka basu gurbin karatu kafin shekarar 2017.Wadanda bayanansu ke tare da shi wa’adin wata daya daga ranar 1 ga Augusta zuwa 31,2024; duk wani gurbin da aka bayar kafin 2017 ba za a amince da shi ba, idan har ba a bayyana hakan ba cikin wata dayan.”

Ya ce an ja kunnen makarantu su yi amfani da umarnin da aka basu, domin kuwa ba za a kara wani wa’adi ba, ba za a sake amincewa da wasu ‘yan makarantar da ba a shigar da bayanansu ba, wadanda ko ma rajista ba su yi da hukumar ba, ba ma a maganar sun rubuta jarabawarta ba’’.

‘’Wannan matakin an dauke shi ne domin ayi maganin yadda ake bada guraben ilimi ba tare da bin ka’ida ba da kuma sa bayanan karya, yayin da da za a rika tabbatar da ana bin dokar CAPS.”

Hakanan hukumar ta nuna rashin jin dadin ta akan abinda ake kira da suna yadda ake bada damar gurbin karatu wato wanda ake yi ko wace rana da wadansu makarantun fasaha da wasu ke yi da hadin bakin wasu Jami’o’i.

Benjamin ya ce “yana da kyau mutane su gane su wadancan nau’oin karatun hukumomin kula da ilimin fasaha da Jami’oi, basu amince da su ba.Dukkansu shigar kutse suke neman su yi ma tsarin ilimin Nijeriya.”

” Wata damfara ce da ake mantawa da masu nagarta kamar yadda tsarin dokar bada guraben karatu ta tanada ga wadanda za su kasance masu zama makaranta,a bi hanyar da bata dace ba wajen amfani da abubuwan da ba kan ka’ida suke ba, domin a samu kudaden da kan ka’ida suke ba. Ta haka sai a bata ma wadanda suke son shiga ta sahiyar hanya, tare da wadanda suke fandararru.

Daliban da basu yi kokarin azo a gani ba ko makin da bai taka kara ya karya ba, lokacin da suka yi jarabawar shiga manyan makarantu, irinsu ne ake jan hankalinsu, su je su yi irin karatun da ko sun kammala zai iya zame masu alakakai.

Ya ce an gano wasu makarantu da suke daukar dalibai da yawa ta hanyar tasarin karatun da ba a amince da shi ba, inda daga karshe su kan hada su tare da wadanda suka zauna a makarantar suke, amma sai su yaye su tare.

Jamb
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Jami’in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

Jami'in MDD Ya Yaba Da Samar Da Fasahar Juncao Don Bunkasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.